ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Raɗɗa Ya Raba Naira Miliyan 20 Ga Iyalan ‘Yan Sintirin Da Suka Rasu A Yaki Da ‘Yan Bindiga

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Gwamna Radda

Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ware kuɗi naira miliyan 20 domin tallafawa iyalan ‘yan sintiri da suka rasa rayukansu a lokacin fafatawa da ‘yan bindiga.

 

Da yake ƙaddamar da bada wannan tallafi, sakataren gwamnatin jihar Katsina Alhaji Abdullahi Garba Faskari ya bayyana cewa, anyi wannan tsari da kyakkyawar niyya domin rage radadin rashin da iyalan jami’an tsaro da ‘yan sintiri suka yi.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

A cewar sa wannan ɗaya ne daga cikin tarin tsare-tsaren da wannan gwamnati take da shi na nuna kauna da tausaya wa ga iyalan waɗanda suka rasa iyalansu da kuma waɗanda suka samu raunuka.

 

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sakataren gwamnatin jihar Katsina ya ƙara da cewa wannan yana daga cikin alkawarin da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ɗauka akan wannan matsala ta tsaro wanda ya ce kullum da abin yake kwana da shi yake tashin.

 

“Idan jama’a ba su manta ba, gwamna Malam Dikko Raɗɗa ya bayyana cewa idan kuɗin jihar Katsina za su ƙare akan matsalar tsaro, to zai tunkare ta tsakaninsa da Allah, kuma ku shaida ne, kwana nan ya amince da kashe Naira biliyan dubu 7.8 akan wannan matsala.” Inji Faskari

 

Haka kuma ya yi kira ga jama’a da su taimakawa jami’an tsaro da bayanan sirri wanda zai taimaka wajan kawo ƙarshen wannan matsala, sannan ya ƙara jaddada cewa kofar wannan gwamnati a buɗe take domin ba

da shawara musamman akan sha’anin tsaro.

 

Shina yake jawabi, mai taimakawa Gwamna Raɗɗa akan waɗanda bala’in ‘yan bindiga ya shafa. Alhaji Sa’idu Ibrahim Danja ya bayyana cewa duk jami’an tsaron ‘yan sintiri sauransu gwamnati ke ɗaukar nauyin yi masu magani idan suka sami raunuka.

 

A cewar sa yanzu haka akwai jami’an tsaro guda 4 da jama’ar gari 32 da suke kwance a asibitin koyarwa ta Katsina da kuma asibitin Ƙashi kuma gwamnatin Malam Dikko Umar Raɗɗa ke ɗaukar nauyin yi masu magani.

 

Ya ƙara da wannan naira miliyan 20 da aka ware an tsara yadda za a rabawa iyalan waɗanda wannan lamari ya shafa su talatin da uku (33) inda ya ce kowace mutum za a baiwa iyalansa naira dubu 500 da kuma iyalan wani jami’in soja da ya rasa ransa za a bashi naira miliyan ɗaya .

 

” Haka kuma muna da jami’an tsaro guda goma da suka samu raunuka wanda kuma za a baiwa kowanne su Naira dubu ɗari biyu da hamsin (250) domin su cigaba da tallafawa iyalan su” inji

 

Daga ƙarshe ya bayyana cewa waɗannan kuɗaɗen da aka ba su ba wai diyya ba ce, tallafi daga gwamna Malam Dikko Raɗɗa kuma wata hanya ce ta ƙara ƙarfafa jami’an tsaro akan wannan aiki na sadaukarwa da suke yi ba dare ba rana.

Gwamna radda
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

Harin 'Yan Bindiga A Kauyen Dan-Umaru: 'Yansanda Sun Kwato Roka A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.