ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Raɗɗa Ya Raba Naira Miliyan 20 Ga Iyalan ‘Yan Sintirin Da Suka Rasu A Yaki Da ‘Yan Bindiga

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Gwamna Radda

Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ware kuɗi naira miliyan 20 domin tallafawa iyalan ‘yan sintiri da suka rasa rayukansu a lokacin fafatawa da ‘yan bindiga.

 

Da yake ƙaddamar da bada wannan tallafi, sakataren gwamnatin jihar Katsina Alhaji Abdullahi Garba Faskari ya bayyana cewa, anyi wannan tsari da kyakkyawar niyya domin rage radadin rashin da iyalan jami’an tsaro da ‘yan sintiri suka yi.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

A cewar sa wannan ɗaya ne daga cikin tarin tsare-tsaren da wannan gwamnati take da shi na nuna kauna da tausaya wa ga iyalan waɗanda suka rasa iyalansu da kuma waɗanda suka samu raunuka.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sakataren gwamnatin jihar Katsina ya ƙara da cewa wannan yana daga cikin alkawarin da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ɗauka akan wannan matsala ta tsaro wanda ya ce kullum da abin yake kwana da shi yake tashin.

 

“Idan jama’a ba su manta ba, gwamna Malam Dikko Raɗɗa ya bayyana cewa idan kuɗin jihar Katsina za su ƙare akan matsalar tsaro, to zai tunkare ta tsakaninsa da Allah, kuma ku shaida ne, kwana nan ya amince da kashe Naira biliyan dubu 7.8 akan wannan matsala.” Inji Faskari

 

Haka kuma ya yi kira ga jama’a da su taimakawa jami’an tsaro da bayanan sirri wanda zai taimaka wajan kawo ƙarshen wannan matsala, sannan ya ƙara jaddada cewa kofar wannan gwamnati a buɗe take domin ba

da shawara musamman akan sha’anin tsaro.

 

Shina yake jawabi, mai taimakawa Gwamna Raɗɗa akan waɗanda bala’in ‘yan bindiga ya shafa. Alhaji Sa’idu Ibrahim Danja ya bayyana cewa duk jami’an tsaron ‘yan sintiri sauransu gwamnati ke ɗaukar nauyin yi masu magani idan suka sami raunuka.

 

A cewar sa yanzu haka akwai jami’an tsaro guda 4 da jama’ar gari 32 da suke kwance a asibitin koyarwa ta Katsina da kuma asibitin Ƙashi kuma gwamnatin Malam Dikko Umar Raɗɗa ke ɗaukar nauyin yi masu magani.

 

Ya ƙara da wannan naira miliyan 20 da aka ware an tsara yadda za a rabawa iyalan waɗanda wannan lamari ya shafa su talatin da uku (33) inda ya ce kowace mutum za a baiwa iyalansa naira dubu 500 da kuma iyalan wani jami’in soja da ya rasa ransa za a bashi naira miliyan ɗaya .

 

” Haka kuma muna da jami’an tsaro guda goma da suka samu raunuka wanda kuma za a baiwa kowanne su Naira dubu ɗari biyu da hamsin (250) domin su cigaba da tallafawa iyalan su” inji

 

Daga ƙarshe ya bayyana cewa waɗannan kuɗaɗen da aka ba su ba wai diyya ba ce, tallafi daga gwamna Malam Dikko Raɗɗa kuma wata hanya ce ta ƙara ƙarfafa jami’an tsaro akan wannan aiki na sadaukarwa da suke yi ba dare ba rana.

Gwamna radda
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

Harin 'Yan Bindiga A Kauyen Dan-Umaru: 'Yansanda Sun Kwato Roka A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.