• English
  • Business News
Thursday, September 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Nemi Taimako Don Gina Gidaje Ga Waɗanda Rikicin Ta’addanci Ya Shafa

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
in Labarai
0
Gwamna Radda Ya Nemi Taimako Don Gina Gidaje Ga Waɗanda Rikicin Ta’addanci Ya Shafa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Umaru Dikko Radda, ya roƙi ƙasashen waje da ƙungiyoyin agaji na duniya da su tallafa wajen gina gidaje masu arha ga iyalan da rikicin ta’addanci da fashi da makami ya raba da muhallansu. Gwamnan ya yi wannan kira ne yayin wani shirin tallafa wa marasa galihu da aka shirya tare da Qatar Charity Nigeria a Katsina.

Ya bayyana cewa har yanzu akwai buƙatar ƙarin gidaje duk da cewa an riga an gina gidaje 152 tare da haɗin gwuiwar United Nations Development Programme (UNDP) don mazauna da suka rasa muhallansu sakamakon rashin tsaro. “Muna da fili da yawa a ƙananan hukumomi da suke buƙatar irin wannan taimako,” in ji shi, yana mai kira ga Qatar Charity da sauran abokan hulɗa na ƙasashen waje da su ƙara sa hannu don tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

  • Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
  • Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Radda ya jaddada cewa duk da muhimmancin taimakon ƙasashen waje, jihar Katsina ma tana ƙarfafa tsarin jin ƙai da zamantakewa. Ya ce gwamnatinsa na saka jari a fannin koyon sana’o’i, da tallafin kuɗi ga ƙananan ƴan kasuwa, da shirye-shiryen a ƙauyuka don rage talauci da kuma ƙarfafa haɗin kai.

Wannan kiran nasa ya zo ne a lokacin da aka raba babura, da injinan ɗinki, da injinan niƙa ga ɗaruruwan gwauraye, da kuma marayu, da marasa galihu a jihar.

Gwamnan ya yaba wa Qatar Charity Nigeria bisa wannan tallafi, yana mai bayyana shi a matsayin hanya ta tallafa wa rayuwa da kuma kawo sauyi. Ya kuma shawarci waɗanda suka amfana da kayan da su yi amfani da su yadda ya kamata domin inganta rayuwarsu, yana mai nanata ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da cewa kowane ɗan jihar ba a bar shi a baya ba.

Labarai Masu Nasaba

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DikkoKatsinaRadda
ShareTweetSendShare
Previous Post

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

Next Post

Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

18 minutes ago
Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki
Manyan Labarai

Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

2 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

3 hours ago
UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro
Manyan Labarai

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗansanda Da Wata Mata, Sun Yi Darkuwa Da Mutum 6 A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗansanda Da Wata Mata, Sun Yi Darkuwa Da Mutum 6 A Kwara

15 hours ago
Ma’aikatan Gwamnati 5,000 Sun Fara Rubuta Jarabawar Tabbacin Gurbin Aiki A Kaduna
Labarai

Ma’aikatan Gwamnati 5,000 Sun Fara Rubuta Jarabawar Tabbacin Gurbin Aiki A Kaduna

16 hours ago
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

September 25, 2025
Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

September 25, 2025
Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

September 25, 2025
Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

September 25, 2025
Gwamna Radda Ya Nemi Taimako Don Gina Gidaje Ga Waɗanda Rikicin Ta’addanci Ya Shafa

Gwamna Radda Ya Nemi Taimako Don Gina Gidaje Ga Waɗanda Rikicin Ta’addanci Ya Shafa

September 25, 2025
UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

September 25, 2025
An Shirya Bikin Kaddamar Da Shirin Gaskiya Na Talabijin “Laszlo Hudec” Cikin Harshen Slovak A Kasar Slovakia

An Shirya Bikin Kaddamar Da Shirin Gaskiya Na Talabijin “Laszlo Hudec” Cikin Harshen Slovak A Kasar Slovakia

September 24, 2025
Xi Ya Jaddada Batun Gina Yankin Xinjiang Na Zamani Mai Ra’ayin Gurguzu

Xi Ya Jaddada Batun Gina Yankin Xinjiang Na Zamani Mai Ra’ayin Gurguzu

September 24, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Mutane Sun Yaba Da Gina “Tsarin Xinjiang” A Turbar Zamanantarwar Kasar Sin 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Mutane Sun Yaba Da Gina “Tsarin Xinjiang” A Turbar Zamanantarwar Kasar Sin 

September 24, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗansanda Da Wata Mata, Sun Yi Darkuwa Da Mutum 6 A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗansanda Da Wata Mata, Sun Yi Darkuwa Da Mutum 6 A Kwara

September 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.