• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Radda Ya Nemi Taimako Don Gina Gidaje Ga Waɗanda Rikicin Ta’addanci Ya Shafa

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago
Radda

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Umaru Dikko Radda, ya roƙi ƙasashen waje da ƙungiyoyin agaji na duniya da su tallafa wajen gina gidaje masu arha ga iyalan da rikicin ta’addanci da fashi da makami ya raba da muhallansu. Gwamnan ya yi wannan kira ne yayin wani shirin tallafa wa marasa galihu da aka shirya tare da Qatar Charity Nigeria a Katsina.

Ya bayyana cewa har yanzu akwai buƙatar ƙarin gidaje duk da cewa an riga an gina gidaje 152 tare da haɗin gwuiwar United Nations Development Programme (UNDP) don mazauna da suka rasa muhallansu sakamakon rashin tsaro. “Muna da fili da yawa a ƙananan hukumomi da suke buƙatar irin wannan taimako,” in ji shi, yana mai kira ga Qatar Charity da sauran abokan hulɗa na ƙasashen waje da su ƙara sa hannu don tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

  • Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
  • Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Radda ya jaddada cewa duk da muhimmancin taimakon ƙasashen waje, jihar Katsina ma tana ƙarfafa tsarin jin ƙai da zamantakewa. Ya ce gwamnatinsa na saka jari a fannin koyon sana’o’i, da tallafin kuɗi ga ƙananan ƴan kasuwa, da shirye-shiryen a ƙauyuka don rage talauci da kuma ƙarfafa haɗin kai.

Wannan kiran nasa ya zo ne a lokacin da aka raba babura, da injinan ɗinki, da injinan niƙa ga ɗaruruwan gwauraye, da kuma marayu, da marasa galihu a jihar.

Gwamnan ya yaba wa Qatar Charity Nigeria bisa wannan tallafi, yana mai bayyana shi a matsayin hanya ta tallafa wa rayuwa da kuma kawo sauyi. Ya kuma shawarci waɗanda suka amfana da kayan da su yi amfani da su yadda ya kamata domin inganta rayuwarsu, yana mai nanata ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da cewa kowane ɗan jihar ba a bar shi a baya ba.

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU
Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro
Labarai

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Next Post
Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai

Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.