• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

by Shehu Yahaya and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Kaduna Sanata Uba Sani, ya bukaci jama’a da su kwantar da hankali kan kashe wani matashi Dan shekara 25 Abubakar Abdullahi Wanda jami’an tsaro suka harba a unguwar Barnawa dake Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu.

 

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin kwanishinan yada labarai na jihar kaduna Malam Ahmed Maiyaki yayin da suka jagoranci jami’an gwamnatin jihar domin jajantawa iyalan matashi marigayi Abubakar Abdullahi a unguwar Barnawa dake cikin Karamar hukumar Kaduna ta kudu.

  • Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani
  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Maiyaki yace tuni gwamna Uba Sani ya bada umarnin a gudanar da bincike domin gano dalilin mutuwar matashin.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

Tun Farko tawagar gwamnatin ta Isa fadar hakimin Barnawa domin isar da sakon ta’aziyyar gwamnatin jihar kaduna na rashin matashi inda suka tabbatar wa da Hakimin cewa gwamnatin jihar kaduna zatayi duk Mai yiwuwa wajen ganin anyiwa matashi Abubakar adalci da kuma gano dalilin mutuwarsa.

 

Hakazalika, tawagar gwamnan sun Kai ziyarar jaje gidan mamacin domin jajantawa iyayensa da ‘yan uwansa .

 

“kwamishinan ya Kara da cewa ‘Mai girma gwamna Uba Sani Yaso yazo da kansa amma bisa wasu abubuwa da suka bijiro hakan ya sanya ya wakilto mu saboda haka gwamna ya kadu matuka da samun labarin rasuwar Abubakar”.

 

Maiyaki, yace domin ganin an dakile matsalar yawaitar tu’ammali da muyagun kwayoyi, gwamnatin jihar Kaduna ta Kafa wani kwamitin hadin gwiwa na jami’an tsaro yaki da masu sha da fataucin muyagun kwayoyi a jihar.

 

Hakazalika, ya bukaci daukacin alummar jihar musamman matasa da su kaucewa tu’ammali da muyagun kwayoyi domin Kara samum zaman lafiya a fadin jihar baki daya.

 

Akan, yayi Kira ga iyaye da matasa da su baiwa jami’an tsaro goyon bayan da suka kamata wajen dakile matsalar shaye-shayen muyagun kwayoyi.

 

Ya kuma jinjinawa kokarin Hakimin Barnawa Alhaji Kabiru Zubairu na Kara hada kan al’umma da wajen tabbatar da zaman lafiya ya Kara sanuwa a garin Barnawa Dama jihar Kaduna baki daya.

 

A nasa jawabin Kwanishinan Ma’aikatar tsaro da harkikin cikin gida na jihar kaduna Barista Suleman Shu’aibu ( SAN) yace zaman lafiya da Samar da tsaro yana daga cikin manyan kudurorin gwamna Uba Sani inda ya bayar da tabbacin cewa zasu ci gaba da duk Mai yiwuwa wajen kare rayuka da dukuyoyin alummar jihar Baki daya.

 

Akan hakan, yayi Kira ga alummar jihar da su ci gaba da baiwa jami’an tsaro goyon bayan da suka kamata wajen ganin an magance matsalar bata gari Wanda hakan zai tqimakawa kokarin gwamnati na kara Samar da ayyukan ci gaba a ciki da wajen jihar.

 

Da yake nasa jawabin hakimin Barnawa kuma Madaucin Arewan Zazzau Alhaji Kabiru Zubairu, yace babu abunda da zasu cewa gwamnatin jihar kaduna sai Fatan alkhairi da samun nasara.

 

Yace alummar Barnawa zasu tabbatar da cewa su ci gaba da marawa gwamnatin Uba Sani baya domin ci gaba da aiwatar da ayyukan da takeyi na ci ga.

 

Anasa jawabin kwamishinan da lamuran cikin gida Barista Suleiman Shu’aibu ( SAN) yace gwamnatin jihar Kaduna bata ji dadin abinda da faru ba inda lamarin ya faru ne bisa kuskure inda Yayi addu’ar Allah ya gafartawa mamacin.

 

A nasa jawabin hakimin Barnawa Alhaji Kabiru Zubairu ( Badauchin Arewan Zazzau) yace tun lokacin da lamarin ya faru jami’an tsaro sun bayar da gudummawa wajen ganin an samu zaman lafiya.

 

‘Wannan yaro da ya rasu jika ne a wurina Saboda ‘ya ta ce ta haife shi saboda haka muna da tabbacin cewa yayi shahada ne. Wannan mataki da gwamnan jihar Kaduna ya dauka na kawo mana gaisuwa bazamu manta da shi saboda ya karrrama mu kwarai da gaske Kuma.

 

Suma iyayen mamacin sun nuna Jin dadinsu da irin matakin da gwamnatin jihar kaduna ta dauka na aiwatar da bincike abin a yaba ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Next Post

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

Related

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

8 minutes ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

53 minutes ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

5 hours ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

6 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

7 hours ago
Next Post
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

September 7, 2025
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

September 7, 2025
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

September 7, 2025
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

September 7, 2025
Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

September 7, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.