ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

by Bashir Aliyu
10 months ago
Tsaro

Tun da aka nada shi a matsayin karamin Ministan Tsaro a 2023, Dakta Bello Matawalle ya sake kawo sabon dabaru ta fannin tsaro, nazari da kuma daukar matakan da suka jibi dasa tubalin ginin sashen tsaro na kasa.

A lokacinsa an samu manyan nasarori a bangaren yaki da ta’addanci, zamanantar da rundunar soja, da kuma tabbatar da zaman lafiyar kasa, wadanda sune suka sa ake kallonsa a matsayin daya daga cikin manyan mutunen da suke bayar da muhimmiyar gudummawa wurin yaki da rashin tsaro.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

A lokacin jagorancinsa ne Ma’aikatar Tsaro ta samu manya-manyan nasarori domin kawo zaman lafiya a kasa. Wadannan nasarori su ne:

ADVERTISEMENT

 

1. Nasarori a kan ta’addanci da satan mutane

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Daya daga cikin manyan nasarorin da Dakta Bello Matawalle ya samu shi ne kaimi da aka yi wurin yaki da ta’addanci, ta hanyar kyautata hadin gwiwa da Sojojin kasa, da Sojojin sama da sauran hukumomin tsaro. An yi rugu-rugu da matattaran ‘yan ta’adda a Arewa Maso Gabas, wanda hakan ya yi sanadiyar raguwar hare-hare. A Arewa Maso Yamma kuwa, gagarumar gudummawa da ma’aikatar tsaro a karkashinsa ta amfani da karfin soja ya yi mummunar illa ga matattarar ‘yan ta’adda wanda hakan ya kyautata fata da al’umma ke da shi cewa an kusan share musu hawaye.

 

2. Kula da walwalar sojoji da karfafa musu gwiwa

Ganin cewa karfin Sojan Nijeriya ya dogara ne a rundunarta, Dakta Bello Matawalle ya inganta hanyoyin walwalar sojojin ta hanyar biyan su kudin alawus a kan lokaci, kyautata matsuguninsu, da kuma samun ingantaccen kiwon lafiya. Wannan ya kara azama wa sojojin da suke gwabza yaki a fagagen fama.

 

3. Zamanantar da Dakarun Sojoji

Ganin bukatar gaggawa da ke akwai na zamanantar da sojojin Nigeriya, Matawalle ya samar da waraka ta hanyar samar da sabbin makamai na zamani, da jirage marasa matuki don tattara bayanai da kuma kayan ayyuka da sojoji ke bukata lokacin yaki.

Wadannan kayayyaki sun inganta dabarun da sojoji ke amfani da su ta hanyar raguwar yawan sojojin da ke rasa rayukansu da kuma karuwar nasarori a duk lokacin da aka fita ba-ta-kashi.

 

4. Raguwar sace-sacen mai da zagon kasa wa tattalin arziki.

Tattalin arzikin Nijeriya ya jima na fama da illar da ake masa sakamakon satan danyen mai a yankin Niger Delta. A karkashin jagorancin Matawalle, an samu karuwar aikace-aikacen da suka hada da hadin gwiwar sojojin ruwa wadanda suka hada da lalata cibiyoyin sace danyen mai wanda hakan ya haifar da aruwar danyen mai da ake fitar da kuma karin kudaden shiga ga kasa.

 

5. Karfafa mu’amala da hadin gwiwa a yankin Afrika da kasa-da-kasa.

Yawancin matsalolin tsaro ya kan wuce iyakar kasa, saboda haka ne Dakta Matawalle bai yi kasa a gwiwa ba wurin daukar matakan kulla kawance da makwabtan asashe irin su Chadi, da Nijar da Kamaru, da sauran kawayen kasashe irin su Amurka, Birtaniya da Tarayyar Turai wanda ya inganta yanda ake tattara bayanai da kuma musayar bayanan sirri. Hakan ya sa ‘yan ta’adda da masu aikata muggan laifuka ke samun wahalar samun maboya.

 

6. Karfafa kere-keren kayan yaki a gida

Bisa umurnin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar na tunanin dogaro da kai a fannin tsaro, Dakta Bello Matawalle ya yi kokarin agaza wa Hukumar Samar da Kayan Yaki ta Nijeriya (DICON) domin kara samar da makaman yaki a gida Nijeriya. Wannan mataki ya rage dogaro da kasashen waje da kuma karfafa tattalin arzikin tsaron Nijeriya.

Baya ga bangaren yaki, Bello Matawalle yana cigaba da jaddada muhimmancin aiki da al’umma domin dawo da tsaro. Wannan kiranye da yake yi wurin neman tattaunawa, da sasanci da kuma ayyukan cigaba a yankunan da ake rikici sun taimaka matuka gaya wajen dinke rashin yarda tsakanin jami’an tsaro da kuma fararen hula, wanda hakan zai haifar da zaman lafiya mai dorewa.

Jagorancin Bello Matawalle ya nuna aiki ba kama kafar yaro, sabbin dabaru, da kuma kishin kasa. Nasarorinsa ya nuna irin fahimtarsa a matsalolin tsaron Nijeriya da kuma irin niyyar da gwamnati ke da shi wurin magance su.

Bashir Aliyu dan jarida ne mai nazarin al’amuran da suka shafi siyasa da tsaro.

Tsaro
Bashir Aliyu
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.