• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

by Sulaiman
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon katunan cirar kuɗi (ATM) ga waɗanda suka ci gajiyar shirye-shiryen tallafi na Bankin Duniya da ake kira ‘Cash Transfer’.

 

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Litinin a Sakatariyar Ƙaramar Hukumar Tsafe.

  • Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
  • Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an tsara shirin ne domin bai wa kowane mutum da ya cin gajiyar shirin tallafin kuɗi N75,000.00.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya sake jaddada cewa bikin ya nuna wani muhimmin mataki a ƙoƙarinsa na ƙarfafa wa al’ummar Zamfara masu ƙaramin ƙarfi.

 

“Saboda haka, cikin farin ciki na tsaya a gabanku domin ƙaddamar da wannan muhimmin shiri.

 

“Ya ku jama’a, da baƙi, an tsara wannan shiri ne domin bayar da tallafin kuɗi na Naira 75,000.00 kowanne ga masu cin gajiyar shirin su 448,141.

 

“Kamar yadda Kwamishina Kainuwa ya bayyana a baya, daga cikin adadin da ake sa ran, mutane 279,534 sun cika mafi ƙarancin abin da ake buƙata don karbar Naira 75,000 kowannen su, sauran waɗanda suka ci gajiyar shirin za a tantance su kuma za a ba su nasu da zarar an kammala, In Sha Allahu.

Zamfara

“Ga waɗanda suka ci gajiyar wannan shirin, ina tunatar da kuma gargaɗar ku da kada ku yi amfani da wannan kuɗi wajen biyan buƙatun cikin gida da aka saba yi, wannan ƙarfafawa ce da nufin ba ku damar saka hannun jari a nan gaba don tallafa wa kanku da iyalanku da kuma bayar da gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikinmu na gida da ma ƙasa baki ɗaya.

 

“Ina kira gare ku da ku yi amfani da wannan damar ta hanyar da ta dace, ku saka hannun jari a harkokin kasuwanci, kuma ku zama masu dogaro da kai.”

 

Gwamnan ya gode wa Gwamnatin Tarayya, da abokan hulɗa, da masu ruwa da tsaki, musamman ma ofishin bayar da tallafin kuɗi na ƙasa, bisa jajircewa da bayar da gagarumar gudunmawa ga shirin.

 

“Bari na yi amfani da wannan dama domin tabbatar muku da cewa gwamnatinmu za ta ci gaba da haɗa kai da kowane mutum ko ƙungiya domin ci gaban jiharmu.

 

“Da wannan nake farin cikin ƙaddamar da raba katunan cirar kuɗi don sauƙaƙe biyan kuɗin Cash Transfer ga waɗanda suka cancanta.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Next Post

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

Related

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

2 hours ago
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin
Manyan Labarai

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

3 hours ago
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

13 hours ago
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
Manyan Labarai

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

18 hours ago
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti
Manyan Labarai

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

23 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu
Manyan Labarai

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

1 day ago
Next Post
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

September 4, 2025
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

September 4, 2025
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.