• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Aikewa Majalisa Sunayen Kwamishinoni 23 Don Tantancesu

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Aikewa Majalisa Sunayen Kwamishinoni 23 Don Tantancesu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya aike wa Majalisa dokokin jihar sunayen mutum ashirin da uku (23) da ya zaba a matsayin Kwamishinoninsa da yake fatan Majalisar za ta tantance tare da amincewa da su a matsayin Kwamishinoni kuma mambobin Majalisar zartaswar jihar. 

 

Wannan matakin an yi ne bisa dogara da sashin doka kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ta 1999 ta tanadar

  • Gwamnatin Bauchi Ta Ware Rawunan Wasu Hakimai 6 Kan Kutsa Kai Cikin Harkokin Siyasa

A yayin zaman Majalisar na ranar Litinin da kakakin Majalisar, Rt. Hon. Abubakar Y Suleiman ya jagoranta ne Majalisar ta samu sakon gwamnan Bala Muhammad da ke neman a amince da zabin da ya yi wa mutanen a matsayin Kwamishinoni.

 

Labarai Masu Nasaba

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Shugaban masu rinkaye na Majalisar, Saleh Hodi Jibir ne ya karanta sakon gwamnan.

 

Kamar yadda yake a jerin sunayen da gwamnan ya aike, karamar hukumar Alkaleri ta samu zababbun Kwamishinoni biyu Maiwada Bello (Geo Barrister) da Ibrahim Gambo; kazalika ita ma karamar hukumar Bauchi ta samu zababbun Kwamishinoni biyu masu suna Mahmoud Babamaji Abubakar da Hon. Danlami Ahmed Kawule; Bogoro: Tsammani Lydia Haruna; Dambam: Ahmed Sarki Jalam; Darazo: Yakubu Ibrahim Hamza; Dass: Usman Santuraki; Ganjuwa: Abdul Hassan; Gamawa: Muhammad Salees; Giade: Dr. Yakubu Adamu.

 

Saura su ne: Jama’are: Usman Abdulkadir Moddibo; Itas/Gadau: Hajara Jibrin Gidado; Katagum: Hon. Farouk Mustapha; Kirfi: Hajara Yakubu Wanka; Misau: Aminu Hammayo; Ningi: Hassan El-Yakub, SAN; Shira: Muhammad Hamisu Shira; da kuma Tafawa Balewa: Silas Madugu.

 

Har-ila-yau a karamar hukumar Tafawa Balewa, gwamnan ya zabo Abubakar Abdulhamid Bununu; sannan, ita ma karamar hukumar Toro ta na da zababbun Kwamishinoni biyu Jamila Muhammad Dahiru da Dr. Adamu Umar Sambo; Warji: Abdulrazak Nuhu Zaki, sai kuma a karamar hukumar Zaki, gwamnan ya zabi Amina Muhammad Katagum a matsayin wacce yake so a matsayin Kwamishinoni.

 

A fadin sanarwar manema labarai da mai magana da yawun kakakin Majalisar, Abdul Ahmad Burra, Hon. Barr. Habibu Umar (Da ke wakiltar mazabar Kirfi) ya bada shawarar Majalisar ta ware ranakun 2, 3 da 4 na watan Augustan 2023 a matsayin ranakun tantance Kwamishinoni. Sai ya samu marawar bayan Hon. Lawan Dauda (Mazabar Sade).

 

Daga nan Majalisar ta amince da ware ranakun 2, 3 da 4 domin aikin tantance zababbun Kwamishinonin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Na Aiki Tukuru Don Rage Radadin Tsadar Man Fetur – Akume

Next Post

Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

Related

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri
Labarai

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

1 hour ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

2 hours ago
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
Labarai

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

4 hours ago
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
Labarai

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

5 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

13 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

14 hours ago
Next Post
Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 16/05/2025

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.