• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Aikewa Majalisa Sunayen Kwamishinoni 23 Don Tantancesu

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Aikewa Majalisa Sunayen Kwamishinoni 23 Don Tantancesu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya aike wa Majalisa dokokin jihar sunayen mutum ashirin da uku (23) da ya zaba a matsayin Kwamishinoninsa da yake fatan Majalisar za ta tantance tare da amincewa da su a matsayin Kwamishinoni kuma mambobin Majalisar zartaswar jihar. 

 

Wannan matakin an yi ne bisa dogara da sashin doka kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ta 1999 ta tanadar

  • Gwamnatin Bauchi Ta Ware Rawunan Wasu Hakimai 6 Kan Kutsa Kai Cikin Harkokin Siyasa

A yayin zaman Majalisar na ranar Litinin da kakakin Majalisar, Rt. Hon. Abubakar Y Suleiman ya jagoranta ne Majalisar ta samu sakon gwamnan Bala Muhammad da ke neman a amince da zabin da ya yi wa mutanen a matsayin Kwamishinoni.

 

Labarai Masu Nasaba

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Shugaban masu rinkaye na Majalisar, Saleh Hodi Jibir ne ya karanta sakon gwamnan.

 

Kamar yadda yake a jerin sunayen da gwamnan ya aike, karamar hukumar Alkaleri ta samu zababbun Kwamishinoni biyu Maiwada Bello (Geo Barrister) da Ibrahim Gambo; kazalika ita ma karamar hukumar Bauchi ta samu zababbun Kwamishinoni biyu masu suna Mahmoud Babamaji Abubakar da Hon. Danlami Ahmed Kawule; Bogoro: Tsammani Lydia Haruna; Dambam: Ahmed Sarki Jalam; Darazo: Yakubu Ibrahim Hamza; Dass: Usman Santuraki; Ganjuwa: Abdul Hassan; Gamawa: Muhammad Salees; Giade: Dr. Yakubu Adamu.

 

Saura su ne: Jama’are: Usman Abdulkadir Moddibo; Itas/Gadau: Hajara Jibrin Gidado; Katagum: Hon. Farouk Mustapha; Kirfi: Hajara Yakubu Wanka; Misau: Aminu Hammayo; Ningi: Hassan El-Yakub, SAN; Shira: Muhammad Hamisu Shira; da kuma Tafawa Balewa: Silas Madugu.

 

Har-ila-yau a karamar hukumar Tafawa Balewa, gwamnan ya zabo Abubakar Abdulhamid Bununu; sannan, ita ma karamar hukumar Toro ta na da zababbun Kwamishinoni biyu Jamila Muhammad Dahiru da Dr. Adamu Umar Sambo; Warji: Abdulrazak Nuhu Zaki, sai kuma a karamar hukumar Zaki, gwamnan ya zabi Amina Muhammad Katagum a matsayin wacce yake so a matsayin Kwamishinoni.

 

A fadin sanarwar manema labarai da mai magana da yawun kakakin Majalisar, Abdul Ahmad Burra, Hon. Barr. Habibu Umar (Da ke wakiltar mazabar Kirfi) ya bada shawarar Majalisar ta ware ranakun 2, 3 da 4 na watan Augustan 2023 a matsayin ranakun tantance Kwamishinoni. Sai ya samu marawar bayan Hon. Lawan Dauda (Mazabar Sade).

 

Daga nan Majalisar ta amince da ware ranakun 2, 3 da 4 domin aikin tantance zababbun Kwamishinonin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Na Aiki Tukuru Don Rage Radadin Tsadar Man Fetur – Akume

Next Post

Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

Related

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

16 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

2 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

2 hours ago
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89
Labarai

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

2 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

5 hours ago
Ministan Tsaro
Labarai

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

7 hours ago
Next Post
Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

LABARAI MASU NASABA

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.