• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Biya Kashi 50 Na Karin Kudin Kujera Ga Alhazan 1652

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Gwamnatin jihar Bauchi a karkashin jagorancin Sanata Bala Muhammad ta tallafa wajen biyan kaso hamsin cikin dari na karin kudin kujerar aikin hajji da hukumar kula da alhazai ta yi ga maniyyata aikin hajjin bana.

Inda gwamnan ya sanar da biyan kashi hamsin cikin naira miliyan 1,918,000 na karin kudin hajji da NAHCON ta yi kan kowace kujerar zuwa aikin hajji. Maniyyata 1652 ne za su amfana, inda kowani maniyyaci zai ci gajiyar tallafin naira dubu N950, 000.

  • An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Benin Domin Tattauna Hanyoyin Karfafa Dangantakar Kasashensu

Idan za a tuna dai, hukumar kula da jin dadin alhazai ta kasa NAHCON, ta sanar da cewa, kowani maniyyacin da ya biya kudin kujera da niyyar sauke farali zuwa kasa mai tsarki a watannin baya, yanzu zai sake biyan naira miliyan 1.9 domin ya cike naira miliyan 4.9 da suka biya da zai zama sama da naira miliyan shida a matsayin kudin kujerar aikin hajjin 2024.

Kwamishinan kula da harkokin addinai na jihar Bauchi, Hon. Yakubu Hamza shi ne ya sanar da matakin karin a wani taron manema labarai da ya kira a ranar Juma’a, inda ya ce, adadin naira N1, 584, 268, 000 ne gwamnan ya biya wajen tallafa wa karin kudin kujerar ga alhazan.

Hamza ya ce wannan abun yabawa ne lura da cewa kudin da aka kara wa alhazan ba kowa zai iya cikawa ba, inda ya shawarci maniyyatan da su nemo rabin kudin su cika domin amfana da tallafin rabi da gwamnan ya musu.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Ya kara da cewa, wannan tallafin kaso hamsin ya hada har da alhazan da gwamnatin jihar ta dauki nauyin aikin hajjinsu, ya ce idan aka hada dukkanin alhazan da suka biya kudin kujera da fari da wanda da gwamnatin jihar ta biya musu, tallafin da gwamnan ya kara zai kai naira N2, 196, 110, 000.

Shi kuma a nasa bangaren, shugaban hukumar kula da jin dadin alhazai na jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris, ya ce, a kowani lokaci gwamna Bala na maida hankali wajen kyautata jin dadi da walwalar maniyyatan jihar.

Ya ce akwai wasu tsare-tsare da aka yi da za su tabbatar da kyautatawa maniyyata tare da jin dadinsu a yayin gudanar da aikin hajji na bana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Zargin Hannu A Ta’addanci: Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Sheikh Gumi Domin Amsa Tambayoyi

Makasudin Gayyata Ta Da Jami’an Tsaro Suka Yi Kan ‘Yan Bindiga – Sheikh Gumi

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version