• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Biya Kashi 50 Na Karin Kudin Kujera Ga Alhazan 1652

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Biya Kashi 50 Na Karin Kudin Kujera Ga Alhazan 1652
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Bauchi a karkashin jagorancin Sanata Bala Muhammad ta tallafa wajen biyan kaso hamsin cikin dari na karin kudin kujerar aikin hajji da hukumar kula da alhazai ta yi ga maniyyata aikin hajjin bana.

Inda gwamnan ya sanar da biyan kashi hamsin cikin naira miliyan 1,918,000 na karin kudin hajji da NAHCON ta yi kan kowace kujerar zuwa aikin hajji. Maniyyata 1652 ne za su amfana, inda kowani maniyyaci zai ci gajiyar tallafin naira dubu N950, 000.

  • An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Benin Domin Tattauna Hanyoyin Karfafa Dangantakar Kasashensu

Idan za a tuna dai, hukumar kula da jin dadin alhazai ta kasa NAHCON, ta sanar da cewa, kowani maniyyacin da ya biya kudin kujera da niyyar sauke farali zuwa kasa mai tsarki a watannin baya, yanzu zai sake biyan naira miliyan 1.9 domin ya cike naira miliyan 4.9 da suka biya da zai zama sama da naira miliyan shida a matsayin kudin kujerar aikin hajjin 2024.

Kwamishinan kula da harkokin addinai na jihar Bauchi, Hon. Yakubu Hamza shi ne ya sanar da matakin karin a wani taron manema labarai da ya kira a ranar Juma’a, inda ya ce, adadin naira N1, 584, 268, 000 ne gwamnan ya biya wajen tallafa wa karin kudin kujerar ga alhazan.

Hamza ya ce wannan abun yabawa ne lura da cewa kudin da aka kara wa alhazan ba kowa zai iya cikawa ba, inda ya shawarci maniyyatan da su nemo rabin kudin su cika domin amfana da tallafin rabi da gwamnan ya musu.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Ya kara da cewa, wannan tallafin kaso hamsin ya hada har da alhazan da gwamnatin jihar ta dauki nauyin aikin hajjinsu, ya ce idan aka hada dukkanin alhazan da suka biya kudin kujera da fari da wanda da gwamnatin jihar ta biya musu, tallafin da gwamnan ya kara zai kai naira N2, 196, 110, 000.

Shi kuma a nasa bangaren, shugaban hukumar kula da jin dadin alhazai na jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris, ya ce, a kowani lokaci gwamna Bala na maida hankali wajen kyautata jin dadi da walwalar maniyyatan jihar.

Ya ce akwai wasu tsare-tsare da aka yi da za su tabbatar da kyautatawa maniyyata tare da jin dadinsu a yayin gudanar da aikin hajji na bana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kammala Taron Dandalin Boao Na 2024 Cikin Nasara

Next Post

Makasudin Gayyata Ta Da Jami’an Tsaro Suka Yi Kan ‘Yan Bindiga – Sheikh Gumi

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

5 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

6 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

7 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

8 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

8 hours ago
Next Post
Zargin Hannu A Ta’addanci: Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Sheikh Gumi Domin Amsa Tambayoyi

Makasudin Gayyata Ta Da Jami’an Tsaro Suka Yi Kan ‘Yan Bindiga – Sheikh Gumi

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.