• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Wa Fursunoni 153 Afuwa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad Abdulkadir, ya yi wa fursunoni 153 da suke zaune a gidan gyaran hali daban-daban a jihar afuwa.

Al’amarin ya gudana a cikin bukukuwan tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya shekaru 62 da suka gabata da aka gudanar.

  • Gwamna Bala Ya Jinjina Wa Takwaransa Na Borno Kan Yaki Da Boko Haram
  • Manufar Ganowa Da Kawar Da Cutar COVID-19 Nan Take Ta Kasar Sin Ta Yi Tasiri In Ji Babban Mashawarci Game Da Kiwon Lafiya

Bala Muhammad wanda ya samu cikakken ikon yin afuwa bisa dogara da sashin doka na 212 (1) da 2 na kundin tsarin mulkin kasa da ya ba shi damar yin afuwar.

Gwamnan wanda a kashin kansa ya dauki alhakin biyan tarar da kotuna suka yanke wa fursunonin, kuma ya bai wa kowane daga cikin ‘yantattun fursoninin kyautar Naira N50,000 domin su fara gudanar da sana’o’in dogaro da kai bayan sake komawarsu cikin al’umma.

Da ya ke mika kyautar kudin ga wadanda suka amfana a gidan gwamnatin jihar, gwamnan ya bayyana cewar afuwa ga fursunoni 153 da aka daure sakamakon aikata laifuka daban-daban ya gudana ne bisa doka da ta ba shi ikon yin hakan.

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

Ya ce, matakin na zuwa ne bayan shawarwarin da kwamitin afuwa da yafiya na jihar ya ba shi, wanda ya ce an duba laifukansu kuma an gano cewa za su zama mutane na kwarai kuma masu amfani a cikin al’umma.

Ya nuna damuwarsa na cewa wasu daga cikin fursunonin a kan dan kankanin kudin tara mutum sai ya shafe tsawon shekaru a daure.

Ya taya fursunonin da aka ‘yanta murna tare da jawo hankalinsu da cewa kada su koma rayuwarsu ta da, ko yin abubuwan da ka iya maidasu gidan yarin, ya nemi su zama mutane na kwarai a cikin al’umma domin jama’a ta amfanesu.

A nasa jawabin, shugaban kwamitin afuwa da yafiya na jihar Bauchi, kuma kwamishinan shari’a na Jihar Barista Abdulhamid Abubakar Bununu ya bayyana cewar an yi zabin wadanda aka yi wa afuwa ne bisa dacewa da cancanta.

Ya ce kudin tara da aka biya, gwamnan ne a kashin kansa ya biya, kuma dukkanin matakan da suka dace a dokance ya cika wajen samar da afuwa ga fursunonin.

Da yake jawabin godiya a madadin dukkanin fursunonin da aka ‘yanta, Saidu Adamu Giade, ya ce abun da gwamnan ya musu ba za su taba mancewa a cikin rayuwarsu ba, ya kuma ce tabbas za su tababtar ba su sake yin wasu laifukan da za su koma gidajen yarin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

October 11, 2025
Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

October 11, 2025
Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

October 11, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

October 11, 2025
Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

October 11, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.