• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Wa Fursunoni 153 Afuwa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Yi Wa Fursunoni 153 Afuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad Abdulkadir, ya yi wa fursunoni 153 da suke zaune a gidan gyaran hali daban-daban a jihar afuwa.

Al’amarin ya gudana a cikin bukukuwan tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya shekaru 62 da suka gabata da aka gudanar.

  • Gwamna Bala Ya Jinjina Wa Takwaransa Na Borno Kan Yaki Da Boko Haram
  • Manufar Ganowa Da Kawar Da Cutar COVID-19 Nan Take Ta Kasar Sin Ta Yi Tasiri In Ji Babban Mashawarci Game Da Kiwon Lafiya

Bala Muhammad wanda ya samu cikakken ikon yin afuwa bisa dogara da sashin doka na 212 (1) da 2 na kundin tsarin mulkin kasa da ya ba shi damar yin afuwar.

Gwamnan wanda a kashin kansa ya dauki alhakin biyan tarar da kotuna suka yanke wa fursunonin, kuma ya bai wa kowane daga cikin ‘yantattun fursoninin kyautar Naira N50,000 domin su fara gudanar da sana’o’in dogaro da kai bayan sake komawarsu cikin al’umma.

Da ya ke mika kyautar kudin ga wadanda suka amfana a gidan gwamnatin jihar, gwamnan ya bayyana cewar afuwa ga fursunoni 153 da aka daure sakamakon aikata laifuka daban-daban ya gudana ne bisa doka da ta ba shi ikon yin hakan.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Ya ce, matakin na zuwa ne bayan shawarwarin da kwamitin afuwa da yafiya na jihar ya ba shi, wanda ya ce an duba laifukansu kuma an gano cewa za su zama mutane na kwarai kuma masu amfani a cikin al’umma.

Ya nuna damuwarsa na cewa wasu daga cikin fursunonin a kan dan kankanin kudin tara mutum sai ya shafe tsawon shekaru a daure.

Ya taya fursunonin da aka ‘yanta murna tare da jawo hankalinsu da cewa kada su koma rayuwarsu ta da, ko yin abubuwan da ka iya maidasu gidan yarin, ya nemi su zama mutane na kwarai a cikin al’umma domin jama’a ta amfanesu.

A nasa jawabin, shugaban kwamitin afuwa da yafiya na jihar Bauchi, kuma kwamishinan shari’a na Jihar Barista Abdulhamid Abubakar Bununu ya bayyana cewar an yi zabin wadanda aka yi wa afuwa ne bisa dacewa da cancanta.

Ya ce kudin tara da aka biya, gwamnan ne a kashin kansa ya biya, kuma dukkanin matakan da suka dace a dokance ya cika wajen samar da afuwa ga fursunonin.

Da yake jawabin godiya a madadin dukkanin fursunonin da aka ‘yanta, Saidu Adamu Giade, ya ce abun da gwamnan ya musu ba za su taba mancewa a cikin rayuwarsu ba, ya kuma ce tabbas za su tababtar ba su sake yin wasu laifukan da za su koma gidajen yarin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MuhammadBauchiFursunoniGidan Gyaran HaliLaifuka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Bala Ya Jinjina Wa Takwaransa Na Borno Kan Yaki Da Boko Haram

Next Post

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

5 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

6 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

8 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

9 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

10 hours ago
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.