ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Wa Fursunoni 153 Afuwa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad Abdulkadir, ya yi wa fursunoni 153 da suke zaune a gidan gyaran hali daban-daban a jihar afuwa.

Al’amarin ya gudana a cikin bukukuwan tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya shekaru 62 da suka gabata da aka gudanar.

  • Gwamna Bala Ya Jinjina Wa Takwaransa Na Borno Kan Yaki Da Boko Haram
  • Manufar Ganowa Da Kawar Da Cutar COVID-19 Nan Take Ta Kasar Sin Ta Yi Tasiri In Ji Babban Mashawarci Game Da Kiwon Lafiya

Bala Muhammad wanda ya samu cikakken ikon yin afuwa bisa dogara da sashin doka na 212 (1) da 2 na kundin tsarin mulkin kasa da ya ba shi damar yin afuwar.

ADVERTISEMENT

Gwamnan wanda a kashin kansa ya dauki alhakin biyan tarar da kotuna suka yanke wa fursunonin, kuma ya bai wa kowane daga cikin ‘yantattun fursoninin kyautar Naira N50,000 domin su fara gudanar da sana’o’in dogaro da kai bayan sake komawarsu cikin al’umma.

Da ya ke mika kyautar kudin ga wadanda suka amfana a gidan gwamnatin jihar, gwamnan ya bayyana cewar afuwa ga fursunoni 153 da aka daure sakamakon aikata laifuka daban-daban ya gudana ne bisa doka da ta ba shi ikon yin hakan.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ce, matakin na zuwa ne bayan shawarwarin da kwamitin afuwa da yafiya na jihar ya ba shi, wanda ya ce an duba laifukansu kuma an gano cewa za su zama mutane na kwarai kuma masu amfani a cikin al’umma.

Ya nuna damuwarsa na cewa wasu daga cikin fursunonin a kan dan kankanin kudin tara mutum sai ya shafe tsawon shekaru a daure.

Ya taya fursunonin da aka ‘yanta murna tare da jawo hankalinsu da cewa kada su koma rayuwarsu ta da, ko yin abubuwan da ka iya maidasu gidan yarin, ya nemi su zama mutane na kwarai a cikin al’umma domin jama’a ta amfanesu.

A nasa jawabin, shugaban kwamitin afuwa da yafiya na jihar Bauchi, kuma kwamishinan shari’a na Jihar Barista Abdulhamid Abubakar Bununu ya bayyana cewar an yi zabin wadanda aka yi wa afuwa ne bisa dacewa da cancanta.

Ya ce kudin tara da aka biya, gwamnan ne a kashin kansa ya biya, kuma dukkanin matakan da suka dace a dokance ya cika wajen samar da afuwa ga fursunonin.

Da yake jawabin godiya a madadin dukkanin fursunonin da aka ‘yanta, Saidu Adamu Giade, ya ce abun da gwamnan ya musu ba za su taba mancewa a cikin rayuwarsu ba, ya kuma ce tabbas za su tababtar ba su sake yin wasu laifukan da za su koma gidajen yarin ba.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.