ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Wa Fursunoni 153 Afuwa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad Abdulkadir, ya yi wa fursunoni 153 da suke zaune a gidan gyaran hali daban-daban a jihar afuwa.

Al’amarin ya gudana a cikin bukukuwan tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya shekaru 62 da suka gabata da aka gudanar.

  • Gwamna Bala Ya Jinjina Wa Takwaransa Na Borno Kan Yaki Da Boko Haram
  • Manufar Ganowa Da Kawar Da Cutar COVID-19 Nan Take Ta Kasar Sin Ta Yi Tasiri In Ji Babban Mashawarci Game Da Kiwon Lafiya

Bala Muhammad wanda ya samu cikakken ikon yin afuwa bisa dogara da sashin doka na 212 (1) da 2 na kundin tsarin mulkin kasa da ya ba shi damar yin afuwar.

ADVERTISEMENT

Gwamnan wanda a kashin kansa ya dauki alhakin biyan tarar da kotuna suka yanke wa fursunonin, kuma ya bai wa kowane daga cikin ‘yantattun fursoninin kyautar Naira N50,000 domin su fara gudanar da sana’o’in dogaro da kai bayan sake komawarsu cikin al’umma.

Da ya ke mika kyautar kudin ga wadanda suka amfana a gidan gwamnatin jihar, gwamnan ya bayyana cewar afuwa ga fursunoni 153 da aka daure sakamakon aikata laifuka daban-daban ya gudana ne bisa doka da ta ba shi ikon yin hakan.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ya ce, matakin na zuwa ne bayan shawarwarin da kwamitin afuwa da yafiya na jihar ya ba shi, wanda ya ce an duba laifukansu kuma an gano cewa za su zama mutane na kwarai kuma masu amfani a cikin al’umma.

Ya nuna damuwarsa na cewa wasu daga cikin fursunonin a kan dan kankanin kudin tara mutum sai ya shafe tsawon shekaru a daure.

Ya taya fursunonin da aka ‘yanta murna tare da jawo hankalinsu da cewa kada su koma rayuwarsu ta da, ko yin abubuwan da ka iya maidasu gidan yarin, ya nemi su zama mutane na kwarai a cikin al’umma domin jama’a ta amfanesu.

A nasa jawabin, shugaban kwamitin afuwa da yafiya na jihar Bauchi, kuma kwamishinan shari’a na Jihar Barista Abdulhamid Abubakar Bununu ya bayyana cewar an yi zabin wadanda aka yi wa afuwa ne bisa dacewa da cancanta.

Ya ce kudin tara da aka biya, gwamnan ne a kashin kansa ya biya, kuma dukkanin matakan da suka dace a dokance ya cika wajen samar da afuwa ga fursunonin.

Da yake jawabin godiya a madadin dukkanin fursunonin da aka ‘yanta, Saidu Adamu Giade, ya ce abun da gwamnan ya musu ba za su taba mancewa a cikin rayuwarsu ba, ya kuma ce tabbas za su tababtar ba su sake yin wasu laifukan da za su koma gidajen yarin ba.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Bita Ga Takwarorinsu Na Saliyo Game Da Yaki Da Cutar Malaria

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.