• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Jigawa Umar Namadi Ya Raba Kayan Makaranta 30,000 Ga Dalibai Mata

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Ilimi
0
Gwamnan Jigawa Umar Namadi Ya Raba Kayan Makaranta 30,000 Ga Dalibai Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya ƙaddamar da rabon riguna 30,000 ga ɗalibai mata a manyan makarantun sakandire da ke faɗin jihar. Taron rabon ya gudana ne a makarantar sakandiren kimiyyar mata ta gwamnati da ke Jahun, wanda ma’aikatar ilimi mai zurfi ta shirya.

Gwamna Namadi ya jaddada fifikon da gwamnatinsa take bayarwa kan ilimin yara mata, wajen samar da kayan sawa kyauta. Ya kuma bayyana cewa ilimi ga ƴaƴa mata a Jigawa kyauta ne tun daga matakin firamare zuwa manyan makarantu, inda ya nuna muhimmancin ilimi ga al’umma.Gwamnan ya kuma yi alkawarin inganta hanyoyin samun ilimi mai sauƙi da inganci.

  • Ramadan: Gwamnatin Jigawa Za Ta Ciyar Da Mutum 171,900 A Kullum Da Azumi – Namadi
  • Obi Na Jam’iyyar Labour Ya Yi Wata Ganawar Sirri Da Tsohon Gwamnan Jigawa Sule Lamido

Namadi ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samar da yanayi mai kyau na ci gaban malamai, tare da himmatuwa wajen ci gaba da ba da horo da sake horarwa don inganta ayyukan koyo da koyarwa.

Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Jigawa Malam Isa Yusuf,  ya yabawa gwamnan bisa wannan shiri da yayi domin zai taimaka wajen zaman ɗalibai mata a makarantu. Ya ƙara da cewa gwamnan ya amince da gyara makarantun mata guda 12, da raba littafan motsa jiki 70,000, da kuma sayo injinan dinki domin taimakawa dalibai su samu sana’o’i daban-daban.

Ɗalibai a aji yayin ɗaukar darasi a Jigawa
Ɗalibai a aji yayin ɗaukar darasi a Jigawa

Shugabar ƙungiyar ANCOPSS ta jihar, Asmau Sulaiman, ta godewa gwamnan bisa tallafin da yake ba wa yara mata a fannin ilmin ƴaƴa mata, ta yadda kowace yarinya a Jigawa za ta iya zuwa makaranta.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

Wasu daga cikin Waɗanda suka ci gajiyar shirin Safiya Danladi da Zainab Ibrahim sun bayyana godiyarsu tare da yin alƙawarin daukar karatunsu da muhimmanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EducationGirlsGirls childIlimiJigawaMakarantaNamadiSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Habasha Ya Kaddamar Da Asibitin Sojoji Na Kasar Da Ya Samu Tallafin Sin

Next Post

Masana Sun Yabawa Rawar Da Sin Ke Takawa Wajen Inganta Ilimi A Afrika

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

5 days ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Ilimi

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

6 days ago
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
Ilimi

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

6 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

6 days ago
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
Ilimi

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

2 weeks ago
Next Post
Masana Sun Yabawa Rawar Da Sin Ke Takawa Wajen Inganta Ilimi A Afrika

Masana Sun Yabawa Rawar Da Sin Ke Takawa Wajen Inganta Ilimi A Afrika

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.