• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Jigawa Umar Namadi Ya Raba Kayan Makaranta 30,000 Ga Dalibai Mata

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Ilimi
0
Gwamnan Jigawa Umar Namadi Ya Raba Kayan Makaranta 30,000 Ga Dalibai Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya ƙaddamar da rabon riguna 30,000 ga ɗalibai mata a manyan makarantun sakandire da ke faɗin jihar. Taron rabon ya gudana ne a makarantar sakandiren kimiyyar mata ta gwamnati da ke Jahun, wanda ma’aikatar ilimi mai zurfi ta shirya.

Gwamna Namadi ya jaddada fifikon da gwamnatinsa take bayarwa kan ilimin yara mata, wajen samar da kayan sawa kyauta. Ya kuma bayyana cewa ilimi ga ƴaƴa mata a Jigawa kyauta ne tun daga matakin firamare zuwa manyan makarantu, inda ya nuna muhimmancin ilimi ga al’umma.Gwamnan ya kuma yi alkawarin inganta hanyoyin samun ilimi mai sauƙi da inganci.

  • Ramadan: Gwamnatin Jigawa Za Ta Ciyar Da Mutum 171,900 A Kullum Da Azumi – Namadi
  • Obi Na Jam’iyyar Labour Ya Yi Wata Ganawar Sirri Da Tsohon Gwamnan Jigawa Sule Lamido

Namadi ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samar da yanayi mai kyau na ci gaban malamai, tare da himmatuwa wajen ci gaba da ba da horo da sake horarwa don inganta ayyukan koyo da koyarwa.

Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Jigawa Malam Isa Yusuf,  ya yabawa gwamnan bisa wannan shiri da yayi domin zai taimaka wajen zaman ɗalibai mata a makarantu. Ya ƙara da cewa gwamnan ya amince da gyara makarantun mata guda 12, da raba littafan motsa jiki 70,000, da kuma sayo injinan dinki domin taimakawa dalibai su samu sana’o’i daban-daban.

Ɗalibai a aji yayin ɗaukar darasi a Jigawa
Ɗalibai a aji yayin ɗaukar darasi a Jigawa

Shugabar ƙungiyar ANCOPSS ta jihar, Asmau Sulaiman, ta godewa gwamnan bisa tallafin da yake ba wa yara mata a fannin ilmin ƴaƴa mata, ta yadda kowace yarinya a Jigawa za ta iya zuwa makaranta.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

Wasu daga cikin Waɗanda suka ci gajiyar shirin Safiya Danladi da Zainab Ibrahim sun bayyana godiyarsu tare da yin alƙawarin daukar karatunsu da muhimmanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EducationGirlsGirls childIlimiJigawaMakarantaNamadiSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Habasha Ya Kaddamar Da Asibitin Sojoji Na Kasar Da Ya Samu Tallafin Sin

Next Post

Masana Sun Yabawa Rawar Da Sin Ke Takawa Wajen Inganta Ilimi A Afrika

Related

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

7 days ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

7 days ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

1 week ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

1 week ago
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya
Ilimi

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

1 week ago
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano
Ilimi

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

1 week ago
Next Post
Masana Sun Yabawa Rawar Da Sin Ke Takawa Wajen Inganta Ilimi A Afrika

Masana Sun Yabawa Rawar Da Sin Ke Takawa Wajen Inganta Ilimi A Afrika

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.