• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

by Abubakar Sulaiman
1 month ago
in Labarai
0
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da korar mataimaka musamman guda biyu daga muƙamansu bayan kwamitocin bincike sun tabbatar da laifuffuka masu nauyi a kansu. Wannan mataki na zuwa ne bayan zarge-zarge da suka shafi sakin wani mai fataucin miyagun ƙwayoyi da kuma satar kayan tallafi.

Daga cikin waɗanda aka sallama akwai Abubakar Umar Sharada, Mataimaki na Musamman kan Shirye-Shiryen Siyasa, wanda kwamitin bincike ya gano shi a matsayin jagoran shirin sakin wanda ake zargi da fataucin miyagun kwayoyi, da Sulaiman Aminu Danwawu. Sharada an umurce shi da ya miƙa duk kayan gwamnati da ke hannunsa kafin ƙarshen ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025, kuma an gargaɗi shi kada ya yi sake ayyana kan shi a matsayin jami’in gwamnati a yanzu.

  • Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
  • Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

Haka kuma, an sallami Tasiu Adamu Al’amin Roba, Mataimaki na Musamman na Ofishin Majalisar Zartarwa, ya fuskanci sallamar ne bayan kama shi da laifin sake sayar da kayan tallafi a shekarar 2024. An gurfanar da shi a gaban kotu kan zargin sata da haɗa baki, kuma an umurce shi ya mika duk dukiyoyin gwamnati da ke hannunsa kafin ranar 11 ga Agusta.

A gefe guda, gwamnatin jihar ta wanke Hon. Musa Ado Tsamiya, Mashawarci na Musamman kan Harkokin Magudanar Ruwa, daga duk wasu zarge-zarge da ake yi masa bayan kwamitin bincike ya tabbatar da rashin laifinsa.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na yaƙi da cin hanci da rashawa tare da jan hankalin duk jami’an gwamnati su kiyaye gaskiya da riƙon amana a aikinsu da rayuwarsu ta ƙashin kai.

Labarai Masu Nasaba

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Next Post

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Related

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
Labarai

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

34 minutes ago
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli
Manyan Labarai

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

5 hours ago
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

6 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

7 hours ago
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

16 hours ago
Next Post
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami'ar Yakubu Gowon, Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

September 20, 2025
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

September 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

September 20, 2025
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

September 20, 2025
Kano

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

September 20, 2025
Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.