• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kebbi Ya Raba Motoci 24 ga ‘Yan Majalisar Jihar

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya raba sabbin motoci kirar Toyota Fortuner Jeep guda 24 ga ‘yan majalisar dokokin jihar, domin kara karfafa musu gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.

Gwamnan wanda ya mika motocin ga kakakin majalisar Hon. Muhammad Usman Ankwai tare da wasu ’yan majalisa a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi, ya bukace su da su yi amfani da motocin ta hanyar da ya kamata.

  • Dubai Ba Ta Dage Haramcin Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza Ba – Fadar Shugaban Kasa
  • Yadda Aka Fara Zaben Fidda Gwani A Amurka

Ya kuma lura cewa motocin za su taimaka matuka wajen taimaka wa ‘yan majalisar wajen gudanar da ayyukansu na majalisa da himma domin ci gaban jihar.

Ya yaba da kyakkyawar alakar aiki da ke tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa, wanda a cewarsa, ya samar da hanyar gudanar da ayyukan raya jihar daban-daban cikin sauki, wadanda ke da alaka kai tsaye ga rayuwar jama’a.

Gwamna Idris ya karfafa gwiwar ‘yan majalisar da su dore da kyakkyawar alakar da ke tsakaninta da jihar domin samun ci gaba cikin sauri da ciyar da jihar a gaba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

“Dole ne na bayyana a nan cewa ina jin dadin zaman lafiya da ke tsakaninmu, ban taba samun sabani da shugaban majalisar ko da mambobinsa ba.

“Wannan, a zahiri ya taimaka mana wajen aiwatar da ayyuka a duk masarautunmu na gargajiya da muke da a fadin jihar don amfanin mutanenmu,” in ji shi.

Gwamnan ya tuna cewa ya saya tare da raba sabbin motoci guda 30 ga jami’an tsaro, 28 ga kwamishinoni da wasu shugabannin hukumomin.

Ya ce: “A yau muna shaidar rabon sabbin motoci kirar Toyoa Fortuner Jeep guda 24 ga ‘yan majalisar dokokin Jihar Kebbi.

Ya ce gwamnatinsa ta zabi sabbin motoci ne domin kaucewa duk wata gazawa wajen gudanar da ayyukansu.

Daga nan sai ya bukaci wadanda suka ci gajiyar motocin da su yi amfani da ababen hawan domin cimma manufar da aka nufa da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi
Manyan Labarai

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

October 22, 2025
Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal
Labarai

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

October 22, 2025
Next Post
Ma’aikatan Shari’a Sun Janye Yajin Aiki A Osun

Ma'aikatan Shari'a Sun Janye Yajin Aiki A Osun

LABARAI MASU NASABA

Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

October 22, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

October 22, 2025
Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

October 22, 2025
Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.