ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

by Leadership Hausa
8 months ago
Gwarzon

Saboda jajircewarsa wajen kawo sauyi, wanzae da zaman lafiya, da kuma zuba jari a fannin ilimi, lafiya da gine-gine, Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya lashe lambar yabo ta Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 na Jaridar Leadership.

Gwamna Lawal, ya yi ƙwazo wajen inganta Jihar Zamfara wadda ta daɗe tana fama da matsalar tsaro.

  • Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci
  • Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Duk da ƙalubalen tsaro, gwamnan ya fifita harkar ilimi da lafiya a mulkinsa.

ADVERTISEMENT

A ƙarƙashin “Zamfara Rescue Projects,” gwamnan ya aiwatar da muhimman ayyuka kamar gina hanyoyi, gyaran makarantu, da sabunta asibitoci a birane da ƙauyuka.

Ɗaya daga cikin manyan nasarorinsa shi ne Tsarin Makarantar Tsangaya, wanda ya haɗa ilimin addinin Musulunci da ilimin zamani.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Wannan tsarin na taimaka wa yara su samu ilimi mai zurfi da zai ba su damar daidaita da tsarin rayuwarsu na yau da kullum.

Makarantun suna da ɗakunan kwana, gidajen malamai, wutar lantarki mai amfani da hasken rana, rijiyoyin burtsatse, kujeru, kayan karatu, da cibiyar koyon sana’o’i kamar ɗinki, sassaƙa, kwamfuta, da sauransu.

Haka kuma, gwamnan ya gyara Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta Jihar Zamfara da kuma Kwalejin Fasaha da Kimiyya ta Zamfara (ZACAS).

A ɓangaren lafiya kuwa, gwamnatinsa ta gyara asibitoci da cibiyoyin lafiya da dama a faɗin jihar.

Don rage mace-macen mata da jarirai a yayin haihuwa, ya ɗauki ƙarin ma’aikatan lafiya, tare da samar da magunguna da kayan aiki, tare d harkar kyautata kiwon lafiya ga mata masu juna biyu da yara kyauta.

Asibitin Ƙwararru na Yeriman Bakura an gyara shi gaba ɗaya tare da samar da kayan aiki na zamani.

Asibitin Gwamnati na Kauran Namoda ma an sabunta shi da kayan gwaje-gwaje, kujerun haihuwa, injinan ECG, da sauran kayan asibiti na zamani.

A Nasarawa Burkullu, an gina sabbin sassa a Asibitin Gwamnati, ciki har da ɗakin agajin gaggawa, ɗakin tiyata, ɗakin haihuwa, ɗakunan jinya na maza da mata, ɗakin gwaje-gwaje, da ɗakin magani.

Haka kuma an samar da masallatai, gidajen ma’aikata, da rijiyoyin burtsatse.

A ƙaramar hukumar Maru, Asibitin Gwamnati ma an gyara shi tare da sanya kayan aiki na zamani.

Gwamnan, ya kuma ƙaddamar da shirin sabunta birane wanda ya haɗa da gyaran manyan hanyoyi da gine-gine a biranen jihar.

A ɓangaren tsaro, Jihar Zamfara ta samu sauƙin yawaitar hare-hare a ’yan shekarun nan.

An rage kashe-kashe da satar mutane sosai.

Wannan ya faru ne saboda ƙirƙirar rundunar ‘Community Protection Guards’ a kowace ƙaramar hukuma 14 da ke jihar.

An zaɓi mutanen ne bayan cikakken bincike da DSS ta jagoranta, sannan aka horar da su don taimaka wa jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan ta’adda.

Gwamnan ya kuma raba motoci 140 ga hukumomin tsaro daban-daban a jihar.

Tarihin Gwamna Dauda Lawal

An haifi Dauda Lawal a ranar 2 ga watan Satumba, 1965 a Jihar Zamfara.

Ya kammala karatunsa na digiri da digiri na biyu a Fannin Siyasa a Jami’ar Ahmadu Bello, da ke Zariya, sannan ya yi digirin digirgir a Fannin Kasuwanci a Jami’ar Usmanu Danfodiyo, da ke Sakkwato.

Hakazalika, ya yi kwasai-kwasai na horo a Harvard Business School, Oxford University, London School of Economics, da Lagos Business School.

Kafin ya shiga siyasa, ya yi aiki a MAMSER, sannan ya yi aiki a Ofishin Jakadancin Nijeriya a Washington DC a matsayin jami’in shige da fice.

Daga baya ya koma aiki a bankin First Bank of Nigeria, inda ya zama Daraktan Ayyukan Jama’a na Arewa.

Ya shiga siyasa a shekarar 2018, inda ya tsaya takarar gwamna a jam’iyyar APC, amma bai yi nasara ba.

A zaɓen 2023, ya tsaya takarar gwamna a jam’iyyar PDP kuma ya lashe zaɓen, tare da Gwamnan Jihar Zamfara.

Gwarzon
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.