• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Zurmi Bisa Harin ‘Yan Bindiga 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Zurmi Bisa Harin ‘Yan Bindiga 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya jajanta wa al’ummomin da hare-haren ‘yan bindiga ya shafa a baya-bayan nan, ya kuma yaba wa sojoji bisa kokarinsu.

Akwai rahotanni masu kyau da yawa na kawar da dimbin ‘yan bindiga a Zamfara da sauran dazuzzukan Arewa maso Yamma.

  • An Shiga Firgici Bayan Sabon Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Gwamnatin Adamawa Ta Rantsar Da Sabbin Kantamomin Raya Karkara 50

A wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Sulaiman Bala Idris ya fitar, gwamna Lawal ya nuna matukar damuwarsa kan hare-haren da aka kai a karamar hukumar Zurmi.

Ya ce duk da hare-haren da ‘yan bindigar ke kai wa, rahotanni masu inganci sun nuna an kawar da fitattun shugabannin ‘yan bindigar da ke aiki a jihar Zamfara.

Sanarwar ta kara da cewa: “Gwamnatin jihar Zamfara ta damu matuka da hare-haren baya-bayan nan da ake kaiwa al’umomin jihar, musamman a kananan hukumomin Zurmi, Maru, da Tsafe.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

“Muna mika ta’aziyyarmu ga daukacin al’ummar karamar hukumar Zurmi, musamman iyalai da ‘yan uwan ​​wadanda suka rasa ‘yan uwansu.

“Gwamnatin jihar za ta bayar da tallafi da kayayyakin agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa, muna so mu tabbatar wa al’ummar Zamfara cewa mun jajirce wajen tabbatar da tsaron lafiyarsu da dukiyoyinsu.

“Muna sane da sadaukarwar da jami’an tsaro suka yi a kokarin da suke na kare rayukan al’umma, gwamnatin jihar za ta ba su duk wani kayan aiki da kuma tallafin da ya dace domin yakar ‘yan fashi, ba za mu huta ba har sai Zamfara ta samu cikakken tsaro.

Gwamna Lawal ya kuma yabawa kokarin jami’an tsaro na kawar da dimbin shugabannin kungiyoyin ‘yan bindiga a fadin jihar.

“Mun samu rahotanni masu kyau na ci gaban da sojoji suka samu a yakin da ake da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, kokarin da jami’an tsaro suka yi da sadaukarwar abin a yaba ne, dole ne mu ba su goyon baya da kuma yi musu addu’a.

“A cewar rahotannin tsaro, sojojin sun yi nasarar kawar da Kachalla Ali Kawaje, sarkin ‘yan bindiga da ya kitsa sace daliban jami’ar tarayya ta Gusau.

“An samu nasarar kawar da barayi a wurare daban-daban da suka hada da Danjibga, dajin ‘Yar tsakuwa, dajin Munhaye, dajin Kauran Zomo, dajin Dansadau, da kauyen Akuzo.

“Wasu daga cikin shugabannin ‘yan bindigan da aka kashe sun hada da Kachalla Jafaru, Kachalla Barume, Kachalla Shehu, Tsoho, Kachalla Yellow Mai Buhu, Yellow Sirajo, da Kachalla Dan Muhammadu.

“Sauran sun hada da Kachalla Makasko, Sanda, Abdulbasiru Ibrahim, Mai Wagumbe, Kachalla Begu, Kwalfa, Ma’aikaci, Yellow Hassan, Umaru Na Bugala, Isyaka Gwarnon Daji, Iliya Babban Kashi, Auta Dan Mai Jan Ido, Yahaya Dan Shama.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harin 'Yan BindigaNejaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwargida Ta Lashe Lambar Yabo 23, Ta Zama Jarimar Shekarar 2023 A Karatun Likitanci A Jami’ar Danfodiyo 

Next Post

Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

Related

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

8 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

9 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

11 hours ago
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba
Manyan Labarai

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

13 hours ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

13 hours ago
Next Post
Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

June 19, 2025
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.