• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Zurmi Bisa Harin ‘Yan Bindiga 

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Zurmi Bisa Harin ‘Yan Bindiga 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya jajanta wa al’ummomin da hare-haren ‘yan bindiga ya shafa a baya-bayan nan, ya kuma yaba wa sojoji bisa kokarinsu.

Akwai rahotanni masu kyau da yawa na kawar da dimbin ‘yan bindiga a Zamfara da sauran dazuzzukan Arewa maso Yamma.

  • An Shiga Firgici Bayan Sabon Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Gwamnatin Adamawa Ta Rantsar Da Sabbin Kantamomin Raya Karkara 50

A wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Sulaiman Bala Idris ya fitar, gwamna Lawal ya nuna matukar damuwarsa kan hare-haren da aka kai a karamar hukumar Zurmi.

Ya ce duk da hare-haren da ‘yan bindigar ke kai wa, rahotanni masu inganci sun nuna an kawar da fitattun shugabannin ‘yan bindigar da ke aiki a jihar Zamfara.

Sanarwar ta kara da cewa: “Gwamnatin jihar Zamfara ta damu matuka da hare-haren baya-bayan nan da ake kaiwa al’umomin jihar, musamman a kananan hukumomin Zurmi, Maru, da Tsafe.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

“Muna mika ta’aziyyarmu ga daukacin al’ummar karamar hukumar Zurmi, musamman iyalai da ‘yan uwan ​​wadanda suka rasa ‘yan uwansu.

“Gwamnatin jihar za ta bayar da tallafi da kayayyakin agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa, muna so mu tabbatar wa al’ummar Zamfara cewa mun jajirce wajen tabbatar da tsaron lafiyarsu da dukiyoyinsu.

“Muna sane da sadaukarwar da jami’an tsaro suka yi a kokarin da suke na kare rayukan al’umma, gwamnatin jihar za ta ba su duk wani kayan aiki da kuma tallafin da ya dace domin yakar ‘yan fashi, ba za mu huta ba har sai Zamfara ta samu cikakken tsaro.

Gwamna Lawal ya kuma yabawa kokarin jami’an tsaro na kawar da dimbin shugabannin kungiyoyin ‘yan bindiga a fadin jihar.

“Mun samu rahotanni masu kyau na ci gaban da sojoji suka samu a yakin da ake da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, kokarin da jami’an tsaro suka yi da sadaukarwar abin a yaba ne, dole ne mu ba su goyon baya da kuma yi musu addu’a.

“A cewar rahotannin tsaro, sojojin sun yi nasarar kawar da Kachalla Ali Kawaje, sarkin ‘yan bindiga da ya kitsa sace daliban jami’ar tarayya ta Gusau.

“An samu nasarar kawar da barayi a wurare daban-daban da suka hada da Danjibga, dajin ‘Yar tsakuwa, dajin Munhaye, dajin Kauran Zomo, dajin Dansadau, da kauyen Akuzo.

“Wasu daga cikin shugabannin ‘yan bindigan da aka kashe sun hada da Kachalla Jafaru, Kachalla Barume, Kachalla Shehu, Tsoho, Kachalla Yellow Mai Buhu, Yellow Sirajo, da Kachalla Dan Muhammadu.

“Sauran sun hada da Kachalla Makasko, Sanda, Abdulbasiru Ibrahim, Mai Wagumbe, Kachalla Begu, Kwalfa, Ma’aikaci, Yellow Hassan, Umaru Na Bugala, Isyaka Gwarnon Daji, Iliya Babban Kashi, Auta Dan Mai Jan Ido, Yahaya Dan Shama.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harin 'Yan BindigaNejaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwargida Ta Lashe Lambar Yabo 23, Ta Zama Jarimar Shekarar 2023 A Karatun Likitanci A Jami’ar Danfodiyo 

Next Post

Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

Related

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

2 hours ago
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

13 hours ago
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
Labarai

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

15 hours ago
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO
Labarai

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

16 hours ago
An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda
Manyan Labarai

An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

18 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
Tsaro

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

20 hours ago
Next Post
Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

May 29, 2025
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

May 28, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.