• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Zurmi Bisa Harin ‘Yan Bindiga 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Zurmi Bisa Harin ‘Yan Bindiga 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya jajanta wa al’ummomin da hare-haren ‘yan bindiga ya shafa a baya-bayan nan, ya kuma yaba wa sojoji bisa kokarinsu.

Akwai rahotanni masu kyau da yawa na kawar da dimbin ‘yan bindiga a Zamfara da sauran dazuzzukan Arewa maso Yamma.

  • An Shiga Firgici Bayan Sabon Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Gwamnatin Adamawa Ta Rantsar Da Sabbin Kantamomin Raya Karkara 50

A wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Sulaiman Bala Idris ya fitar, gwamna Lawal ya nuna matukar damuwarsa kan hare-haren da aka kai a karamar hukumar Zurmi.

Ya ce duk da hare-haren da ‘yan bindigar ke kai wa, rahotanni masu inganci sun nuna an kawar da fitattun shugabannin ‘yan bindigar da ke aiki a jihar Zamfara.

Sanarwar ta kara da cewa: “Gwamnatin jihar Zamfara ta damu matuka da hare-haren baya-bayan nan da ake kaiwa al’umomin jihar, musamman a kananan hukumomin Zurmi, Maru, da Tsafe.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

“Muna mika ta’aziyyarmu ga daukacin al’ummar karamar hukumar Zurmi, musamman iyalai da ‘yan uwan ​​wadanda suka rasa ‘yan uwansu.

“Gwamnatin jihar za ta bayar da tallafi da kayayyakin agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa, muna so mu tabbatar wa al’ummar Zamfara cewa mun jajirce wajen tabbatar da tsaron lafiyarsu da dukiyoyinsu.

“Muna sane da sadaukarwar da jami’an tsaro suka yi a kokarin da suke na kare rayukan al’umma, gwamnatin jihar za ta ba su duk wani kayan aiki da kuma tallafin da ya dace domin yakar ‘yan fashi, ba za mu huta ba har sai Zamfara ta samu cikakken tsaro.

Gwamna Lawal ya kuma yabawa kokarin jami’an tsaro na kawar da dimbin shugabannin kungiyoyin ‘yan bindiga a fadin jihar.

“Mun samu rahotanni masu kyau na ci gaban da sojoji suka samu a yakin da ake da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, kokarin da jami’an tsaro suka yi da sadaukarwar abin a yaba ne, dole ne mu ba su goyon baya da kuma yi musu addu’a.

“A cewar rahotannin tsaro, sojojin sun yi nasarar kawar da Kachalla Ali Kawaje, sarkin ‘yan bindiga da ya kitsa sace daliban jami’ar tarayya ta Gusau.

“An samu nasarar kawar da barayi a wurare daban-daban da suka hada da Danjibga, dajin ‘Yar tsakuwa, dajin Munhaye, dajin Kauran Zomo, dajin Dansadau, da kauyen Akuzo.

“Wasu daga cikin shugabannin ‘yan bindigan da aka kashe sun hada da Kachalla Jafaru, Kachalla Barume, Kachalla Shehu, Tsoho, Kachalla Yellow Mai Buhu, Yellow Sirajo, da Kachalla Dan Muhammadu.

“Sauran sun hada da Kachalla Makasko, Sanda, Abdulbasiru Ibrahim, Mai Wagumbe, Kachalla Begu, Kwalfa, Ma’aikaci, Yellow Hassan, Umaru Na Bugala, Isyaka Gwarnon Daji, Iliya Babban Kashi, Auta Dan Mai Jan Ido, Yahaya Dan Shama.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harin 'Yan BindigaNejaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwargida Ta Lashe Lambar Yabo 23, Ta Zama Jarimar Shekarar 2023 A Karatun Likitanci A Jami’ar Danfodiyo 

Next Post

Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

4 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

6 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

7 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

8 hours ago
Next Post
Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

Firaministan Jamhuriyar Kongo: Ko Da Yaushe Kasar Sin Ba Ta Dakatar Da Tallafi Da Goyon Baya

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.