• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ofishin Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaro

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ofishin Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Zamfara, ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal, ta ƙaddamar da ofishin amintattun Asusun Kula da Harkokin Tsaro domin daƙile ayyukan ’yan bindiga da sauran ta’addanci a jihar, inda Gwamnan ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tallafa wa asusun ta kowane fanni.

A ranar Juma’ar Gwamna Lawal ya jagoranci ƙaddamar da ginin amintattun Asusun Kula da Harkokin Tsaro da ke Gusau babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce asusun tsaron na Zamfara yana ƙarƙashin jagorancin Tsohon Sufeto Janar na ’yan sanda, MD Abubakar ne.

  • Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

 

A cewar sanarwar, an ƙaddamar da aikin ne a ƙarƙashin wani kwamitin amintattu na ƙwararru a fannin tsaro domin aiwatar da aikin yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

A yayin bikin ƙaddamar da ginin, Gwamna Lawal ya buƙaci sauran jihohin ƙasar nan da su kafa irin waɗannan asusun amintattu, da daidaita tsare-tsare, da samar da tsarin da ya shafi tsaron yankin.

Ya ce, “Yayin da Asusun Tallafa wa Tsaro ya fara aiki cikin tsari, ina roƙon a haɗa hannu da irin waɗannan asusu da wasu jihohi ke kafawa a yankunan su domin haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen daƙile matsalar tsaro.

“Asusun yana da abubuwa da yawa da zai yi yayin da ya fara aiki. Wani abin da asusun zai ƙara mayar da hankali a kai shi ne tabbatar da cire wa yaranmu da matasanmu tunanin rikice-rikice da kuma nuna ƙabilanci, wanda hakan ke haifar da tayar da ƙayar baya a wasu al’ummomi. Wannan ya zama dole don samun ci gaba mai ma’ana kuma mai ɗorewa.

“A ƙarƙashin jagoranci mai nagarta na Shugaban Asusun, IGP M.D Abubakar (Mai Ritaya) da sauran jiga-jigan kwamitin amintattun, muna sa ido ga haɗin kanku don haɓaka rayuwar jama’armu nan take.

“Mun dogara da ku, domin mun san ku duka kuna da cancantar ɗaukar irin wannan nauyi. Na gode da hidimar ku da aikin ku ga jihar ku.

“Abin da ke faɗo min rai a duk lokacin da aka kai wani hari, shi ne yabo bisa ƙoƙarin da Rundunar Kare Jama’a ta Zamfara, wacce muka ƙaddamar kwanan nan take yi wajen ceto al’umma.

“Muna da niyyar ci gaba da ƙoƙari wajen haɗa kan al’umma, ci gaba da wayar da kan jama’a, da kuma tabbatar da bin ƙa’idojin aiki da dukkan mambobin Rundunar Kare Jama’a ta Zamfara suka rantse a kai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GiniJihar ZamfaraOfishiTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sakataren Tsaron Amurka Ya Amince Da Samun “Kudin Yaki” A Fili

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yammata Masu Yawon Dare A Yamai

Related

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

2 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

6 hours ago
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina
Labarai

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

7 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

8 hours ago
Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

18 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

19 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke ‘Yammata Masu Yawon Dare A Yamai

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yammata Masu Yawon Dare A Yamai

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.