• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Tallafa Wa Yara Mata 8,225 Da Ke Sakandare

by Sulaiman and Hussein Yero
4 hours ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Tallafa Wa Yara Mata 8,225 Da Ke Sakandare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya raba tallafin kuɗi ga yara mata 8,225 a dukkanin ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

A ranar Larabar da ta gabata ne gwamnan ya fara rabon kuɗaɗe na ayyukan ACRESAL da Agile a ɗakin taro na Garba Nadama da ke sakatariyar J.B Yakubu a Gusau.

  • Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (3)
  • Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an zabo ‘yan matan sakandaren 8,225 ne daga gidajen masu ƙaramin ƙarfi da marasa galihu.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Kaduna: An Horar Da Sarakunan Gargajiya Kan Sasanta Rikici Da Samar Da Zaman Lafiya

Sanarwar ta ƙara da cewa, kowace yarinya za ta karbi tallafin Naira 40,000 don ci gaba da yi musu rajista da shiga makaranta.

 

“Ƙarin Naira dubu goma-goma da za a bayar na zangon karatu na biyu da na uku zai kawo adadin tallafin zuwa Naira 60,000 ga kowace ɗaliba wanda za a bayar ta bangaren iyaye ko masu kula da su, an amince da Naira Miliyan Ɗari Uku da Ashirin da Biyu ga wannan Kashi na Farko, a halin yanzu ana ci gaba da shirye-shiryen kashi na biyu ga masu cin gajiyar shirin.

 

A wajen bikin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, taron a alamance yana bayar da tallafin kuɗi ne ga waɗanda suka ci gajiyar ayyukan ACReSAL da AGILE, waɗanda suka yi daidai da yadda gwamnatinsa ta mayar da hankali kan ilimi, ci gaba, da kare al’umma, da kuma kare muhalli.

 

Ya ce: “A ƙarƙashin wannan shiri na ACRESAL, mun bayar da tallafin ne ta Asusun Tallafawa Al’umma ga mutum 500 da suka amfana a Gusau, Bungudu, da Kaura Namoda da nufin tallafa wa ayyukan da suka shafi muhalli da tattalin arziki, wanda hakan ke nuni da ƙudurinmu na yaƙi da gurbacewar ƙasa, da inganta noma da inganta rayuwar al’umma a cikin matsalolin da ake fuskanta.

 

“Al’ummar mu na fuskantar wahalhalu kamar fafutukar mata wajen gina ƙananan sana’o’i, matasa masu neman tallafi. Asusun Tallafawa Al’umma yana ba da tallafi mai ɗorewa don tallafawa ci gaba, wanda ke nuna alamar juriya da riƙon amana. Ina kira ga masu cin gajiyar da su yi amfani da wannan tallafin cikin hikima da gaskiya, tare da tabbatar da sakamako na aminci a bayyane, sakamako mai kyau.

 

“Za a ta ci gaba da bayar da tallafin a cikin al’ummomi, ta hanyar amfani da mutane da yawa a tsawon lokaci. Ta hanyar amfani da shi yadda ya kamata, wannan shirin zai ba da misali na hada-hadar kuɗi da ɗorewar tattalin arziki.”

 

Gwamnan ya ci gaba da cewa har yanzu ilimi shi ne babban fifikon gwamnatin sa.

 

“Mun himmatu wajen ganin mun magance tare da shawo kan duk wani shingen da ya shafi tattalin arziki, ababen more rayuwa, ko zamantakewa, waɗanda ke hana ‘ya’yanmu mata samun damar karatu da kuma kammala karatunsu, domin idan ka ilimantar da ’ya mace ko ka karantar da ƙauye ne, domin waɗannan ‘yan mata masu ilimi su na girma zuwa mata masu ƙarfin gwiwa, waɗanda suke ɗaukaka iyalansu, ƙarfafa al’umma, da kuma kawo ci gaba a jiharmu.

 

“Ina yaba wa dukkanin ƙungiyoyin da suka aiwatar da aikin a ƙarƙashin Ma’aikatar Muhalli da Albarkatun Masa da Ma’aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha, da kuma abokan aikinmu na fasaha, saboda sadaukarwa da haɗin gwiwarsu wajen aiwatar da waɗannan muhimman shirye-shirye.

 

“Bari na tabbatar wa mutanen jihar Zamfara cewa wannan gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da manufofi da tsare-tsare masu ma’ana, musamman tun daga tushe, muna ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da gaskiya da kuma yi wa jama’armu hidima.

 

“Ga waɗanda suka ci gajiyar waɗannan tsare-tsare, ku tuna cewa abin da ku ke karba a yau iri ne. Ina roƙon ku da ku raya shi, ku shuka shi, kuma ku bar shi ya zama bishiyar canji ga iyalanku da al’ummominku.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (3)

Next Post

Tinubu Ya Kammala Hanyoyi 420 A Sassan Nijeriya Cikin Shekara 2

Related

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

36 minutes ago
'Yan Bindiga
Labarai

Kaduna: An Horar Da Sarakunan Gargajiya Kan Sasanta Rikici Da Samar Da Zaman Lafiya

1 hour ago
Rashin Halartar Gwamnoni Taron Yi Wa Tsarin Mulki Kwaskwarima A Kaduna Ya Haifar Da Cece-kuce
Labarai

Rashin Halartar Gwamnoni Taron Yi Wa Tsarin Mulki Kwaskwarima A Kaduna Ya Haifar Da Cece-kuce

2 hours ago
yola
Labarai

Tinubu Ya Kammala Hanyoyi 420 A Sassan Nijeriya Cikin Shekara 2

3 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Manyan Jami’an ‘Yansanda 150 Ke Fuskantar Kwamitin Ladabtarwa

5 hours ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

6 hours ago
Next Post
yola

Tinubu Ya Kammala Hanyoyi 420 A Sassan Nijeriya Cikin Shekara 2

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

July 18, 2025
'Yan Bindiga

Kaduna: An Horar Da Sarakunan Gargajiya Kan Sasanta Rikici Da Samar Da Zaman Lafiya

July 18, 2025
Rashin Halartar Gwamnoni Taron Yi Wa Tsarin Mulki Kwaskwarima A Kaduna Ya Haifar Da Cece-kuce

Rashin Halartar Gwamnoni Taron Yi Wa Tsarin Mulki Kwaskwarima A Kaduna Ya Haifar Da Cece-kuce

July 18, 2025
yola

Tinubu Ya Kammala Hanyoyi 420 A Sassan Nijeriya Cikin Shekara 2

July 18, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Tallafa Wa Yara Mata 8,225 Da Ke Sakandare

Gwamnan Zamfara Ya Tallafa Wa Yara Mata 8,225 Da Ke Sakandare

July 18, 2025
Manzon Allah

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (3)

July 18, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Manyan Jami’an ‘Yansanda 150 Ke Fuskantar Kwamitin Ladabtarwa

July 18, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

July 18, 2025
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

July 18, 2025
Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

July 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.