ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Tallafa Wa Yara Mata 8,225 Da Ke Sakandare

by Sulaiman and Hussein Yero
12 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya raba tallafin kuɗi ga yara mata 8,225 a dukkanin ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

A ranar Larabar da ta gabata ne gwamnan ya fara rabon kuɗaɗe na ayyukan ACRESAL da Agile a ɗakin taro na Garba Nadama da ke sakatariyar J.B Yakubu a Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (3)
  • Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an zabo ‘yan matan sakandaren 8,225 ne daga gidajen masu ƙaramin ƙarfi da marasa galihu.

 

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Sanarwar ta ƙara da cewa, kowace yarinya za ta karbi tallafin Naira 40,000 don ci gaba da yi musu rajista da shiga makaranta.

 

“Ƙarin Naira dubu goma-goma da za a bayar na zangon karatu na biyu da na uku zai kawo adadin tallafin zuwa Naira 60,000 ga kowace ɗaliba wanda za a bayar ta bangaren iyaye ko masu kula da su, an amince da Naira Miliyan Ɗari Uku da Ashirin da Biyu ga wannan Kashi na Farko, a halin yanzu ana ci gaba da shirye-shiryen kashi na biyu ga masu cin gajiyar shirin.

 

A wajen bikin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, taron a alamance yana bayar da tallafin kuɗi ne ga waɗanda suka ci gajiyar ayyukan ACReSAL da AGILE, waɗanda suka yi daidai da yadda gwamnatinsa ta mayar da hankali kan ilimi, ci gaba, da kare al’umma, da kuma kare muhalli.

 

Ya ce: “A ƙarƙashin wannan shiri na ACRESAL, mun bayar da tallafin ne ta Asusun Tallafawa Al’umma ga mutum 500 da suka amfana a Gusau, Bungudu, da Kaura Namoda da nufin tallafa wa ayyukan da suka shafi muhalli da tattalin arziki, wanda hakan ke nuni da ƙudurinmu na yaƙi da gurbacewar ƙasa, da inganta noma da inganta rayuwar al’umma a cikin matsalolin da ake fuskanta.

 

“Al’ummar mu na fuskantar wahalhalu kamar fafutukar mata wajen gina ƙananan sana’o’i, matasa masu neman tallafi. Asusun Tallafawa Al’umma yana ba da tallafi mai ɗorewa don tallafawa ci gaba, wanda ke nuna alamar juriya da riƙon amana. Ina kira ga masu cin gajiyar da su yi amfani da wannan tallafin cikin hikima da gaskiya, tare da tabbatar da sakamako na aminci a bayyane, sakamako mai kyau.

 

“Za a ta ci gaba da bayar da tallafin a cikin al’ummomi, ta hanyar amfani da mutane da yawa a tsawon lokaci. Ta hanyar amfani da shi yadda ya kamata, wannan shirin zai ba da misali na hada-hadar kuɗi da ɗorewar tattalin arziki.”

 

Gwamnan ya ci gaba da cewa har yanzu ilimi shi ne babban fifikon gwamnatin sa.

 

“Mun himmatu wajen ganin mun magance tare da shawo kan duk wani shingen da ya shafi tattalin arziki, ababen more rayuwa, ko zamantakewa, waɗanda ke hana ‘ya’yanmu mata samun damar karatu da kuma kammala karatunsu, domin idan ka ilimantar da ’ya mace ko ka karantar da ƙauye ne, domin waɗannan ‘yan mata masu ilimi su na girma zuwa mata masu ƙarfin gwiwa, waɗanda suke ɗaukaka iyalansu, ƙarfafa al’umma, da kuma kawo ci gaba a jiharmu.

 

“Ina yaba wa dukkanin ƙungiyoyin da suka aiwatar da aikin a ƙarƙashin Ma’aikatar Muhalli da Albarkatun Masa da Ma’aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha, da kuma abokan aikinmu na fasaha, saboda sadaukarwa da haɗin gwiwarsu wajen aiwatar da waɗannan muhimman shirye-shirye.

 

“Bari na tabbatar wa mutanen jihar Zamfara cewa wannan gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da manufofi da tsare-tsare masu ma’ana, musamman tun daga tushe, muna ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da gaskiya da kuma yi wa jama’armu hidima.

 

“Ga waɗanda suka ci gajiyar waɗannan tsare-tsare, ku tuna cewa abin da ku ke karba a yau iri ne. Ina roƙon ku da ku raya shi, ku shuka shi, kuma ku bar shi ya zama bishiyar canji ga iyalanku da al’ummominku.”

Zamfara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Zamfara
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
yola

Tinubu Ya Kammala Hanyoyi 420 A Sassan Nijeriya Cikin Shekara 2

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.