• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar

by Sulaiman
6 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya yaba da ƙoƙarin da sojojin Nijeriya ke yi na kai hare-hare kan ’yan bindiga ba ƙaƙƙautawa a jihar.

A ƙarshen makon da ya gabata ne rundunar sojin saman Nijeriya ta kai wani samame kan ’yan bindigar da ke yunƙurin kai hari a ƙauyukan ƙananan hukumomin Zurmi da Maradun.

  • Hukumar CDC Ta Karyata Barkewar Sabbin Cututtuka Masu Yaduwa A Sin
  • An Nemi Sojoji Su Kara Jajircewa Wajen Gudanar Da Ayukansu

A wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Gusau, kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya jajanta wa iyalan fararen hula da harin da jirgin sama ya rutsa da su a Tungar Kara da ke ƙaramar hukumar Zurmi.

Sanarwar ta ƙara da cewa, fararen hular da suka rasa rayukansu ’yan sintiri ne na yankin da aka yi zaton cewa ‘yan bindigar da suka tsere ne daga Gidan Makera a gundumar Boko a ƙaramar hukumar Zurmi.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Mun samu rahotanni masu inganci da yawa na farmakin da rundunar sojin sama ta Operation Fansar Yamma ta kai a ƙarshen mako a ƙananan hukumomin Maradun da Zurmi da ke fama da rikicin ’yan bindiga.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Zamfara

“Wannan farmakin da sojoji suke kaiwa ya rage wa ‘yan bindigar ƙwarin gwiwa matuƙa, ya kuma nuna aniyar rundunar sojojin saman Nijeriya na gudanar da aikin da Kundin Tsarin Mulkin ƙasar ya ba su na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

“A matsayinmu na gwamnati mai kishin ƙasa, muna tabbatar wa ɗaukacin al’ummar jihar cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta tsaya tsayin daka wajen ganin ta ci gaba da samun nasarori a yaƙi da ’yan bindiga. Nasarar da aka samu a baya-bayan nan na nuni da cewa ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro na jiha da na tarayya ya haifar da sakamako mai kyau.

“A bisa waɗannan nasarorin da aka samu, gwamnatin jihar ta sake jaddada aniyar ta na bayar da dukkanin tallafin da ya kamata ga rundunar sojin saman Nijeriya da sauran hukumomin tsaro domin ci gaba da gudanar da ayyukansu da kuma samar da zaman lafiya mai gorewa a jihar.

“Za mu ci gaba da ba da tallafi don inganta musayar bayanan sirri, samar da dabaru, da kuma ƙarfafa cuɗanyar da jama’a da jami’an tsaro, duk a bisa tsarin da ya dace na tabbatar da tsaro da kuma cimma burin maido da zaman lafiya a dukkan sassan jihar.

“Abin takaici, harin ya shafi wasu ’yan sintiri (JTF) a yayin farmakin a Tungar Kara, wanda ya yi sanadin asarar rayuka. Muna roƙon Allah Ta’ala ya saka musu da gidan Aljannah.

“Gwamnatin jihar na miƙa ta’aziyyarta ga iyalan jami’an JTF da suka mutu tare da ba su tabbacin cewa sadaukarwar da mamatan suka yi ba zai tafi a banza ba. Gwamnati za ta ba da tallafi da taimakon da ya dace ga iyalan waɗanda suka rasu.

Zamfara

“A ƙarshe, gwamnati na kira ga jama’a da su lura, su kai rahoton duk wani motsin da ba su gane masa ba, sannan su ba jami’an tsaro cikakken haɗin kai. Ta hanyar haɗin kai za a iya samun nasarar yaƙi da ‘yan bindiga tare da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Zamfara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

Next Post

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Manoma 40 A Borno

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

10 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

1 day ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 day ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Masallata Sun Kuɓuta Daga Harin Ƙunar Baƙin Wake A Jihar Borno

'Yan Ta'adda Sun Kashe Manoma 40 A Borno

LABARAI MASU NASABA

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.