• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar

by Sulaiman
6 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Yaba Wa Rundunar Tsaro Tare Da Jajanta Wa Al’ummar Da Harin Jirgin Sojin Ya Shafa A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya yaba da ƙoƙarin da sojojin Nijeriya ke yi na kai hare-hare kan ’yan bindiga ba ƙaƙƙautawa a jihar.

A ƙarshen makon da ya gabata ne rundunar sojin saman Nijeriya ta kai wani samame kan ’yan bindigar da ke yunƙurin kai hari a ƙauyukan ƙananan hukumomin Zurmi da Maradun.

  • Hukumar CDC Ta Karyata Barkewar Sabbin Cututtuka Masu Yaduwa A Sin
  • An Nemi Sojoji Su Kara Jajircewa Wajen Gudanar Da Ayukansu

A wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Gusau, kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya jajanta wa iyalan fararen hula da harin da jirgin sama ya rutsa da su a Tungar Kara da ke ƙaramar hukumar Zurmi.

Sanarwar ta ƙara da cewa, fararen hular da suka rasa rayukansu ’yan sintiri ne na yankin da aka yi zaton cewa ‘yan bindigar da suka tsere ne daga Gidan Makera a gundumar Boko a ƙaramar hukumar Zurmi.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Mun samu rahotanni masu inganci da yawa na farmakin da rundunar sojin sama ta Operation Fansar Yamma ta kai a ƙarshen mako a ƙananan hukumomin Maradun da Zurmi da ke fama da rikicin ’yan bindiga.

Labarai Masu Nasaba

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

Zamfara

“Wannan farmakin da sojoji suke kaiwa ya rage wa ‘yan bindigar ƙwarin gwiwa matuƙa, ya kuma nuna aniyar rundunar sojojin saman Nijeriya na gudanar da aikin da Kundin Tsarin Mulkin ƙasar ya ba su na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

“A matsayinmu na gwamnati mai kishin ƙasa, muna tabbatar wa ɗaukacin al’ummar jihar cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta tsaya tsayin daka wajen ganin ta ci gaba da samun nasarori a yaƙi da ’yan bindiga. Nasarar da aka samu a baya-bayan nan na nuni da cewa ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro na jiha da na tarayya ya haifar da sakamako mai kyau.

“A bisa waɗannan nasarorin da aka samu, gwamnatin jihar ta sake jaddada aniyar ta na bayar da dukkanin tallafin da ya kamata ga rundunar sojin saman Nijeriya da sauran hukumomin tsaro domin ci gaba da gudanar da ayyukansu da kuma samar da zaman lafiya mai gorewa a jihar.

“Za mu ci gaba da ba da tallafi don inganta musayar bayanan sirri, samar da dabaru, da kuma ƙarfafa cuɗanyar da jama’a da jami’an tsaro, duk a bisa tsarin da ya dace na tabbatar da tsaro da kuma cimma burin maido da zaman lafiya a dukkan sassan jihar.

“Abin takaici, harin ya shafi wasu ’yan sintiri (JTF) a yayin farmakin a Tungar Kara, wanda ya yi sanadin asarar rayuka. Muna roƙon Allah Ta’ala ya saka musu da gidan Aljannah.

“Gwamnatin jihar na miƙa ta’aziyyarta ga iyalan jami’an JTF da suka mutu tare da ba su tabbacin cewa sadaukarwar da mamatan suka yi ba zai tafi a banza ba. Gwamnati za ta ba da tallafi da taimakon da ya dace ga iyalan waɗanda suka rasu.

Zamfara

“A ƙarshe, gwamnati na kira ga jama’a da su lura, su kai rahoton duk wani motsin da ba su gane masa ba, sannan su ba jami’an tsaro cikakken haɗin kai. Ta hanyar haɗin kai za a iya samun nasarar yaƙi da ‘yan bindiga tare da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Zamfara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

Next Post

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Manoma 40 A Borno

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

35 minutes ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

2 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

12 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

13 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

14 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

16 hours ago
Next Post
Masallata Sun Kuɓuta Daga Harin Ƙunar Baƙin Wake A Jihar Borno

'Yan Ta'adda Sun Kashe Manoma 40 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.