• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada cewa gwamnati da kafafen yaɗa labarai abokan hulɗa ne wajen gina ƙasa, ba ‘yan adawa ba, duk da saɓanin da ake samu a wasu lokuta.

 

Ya bayyana haka ne a yayin ziyarar ban-girma da tawagar gudanarwar kamfanin jaridun The Guardian suka kai ofishin sa ranar Alhamis.

  • Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki
  • Mene Ne Ainihin Abun Da Philippines Ta Samu Daga Wajen Amurka?

“Ban yi imani da cewa gwamnati da ‘yan jarida ‘yan adawa ne ba, a’a, abokan hulɗa ne a cikin wannan aiki mai wuyar gaske na gina ƙasa, aikin da ke zuwa da mabanbantan ra’ayoyi da hanyoyi daban-daban,” inji Idris.

 

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Ya bayyana irin rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa a matsayin masu sa ido kan al’umma, inda ya jaddada aikinsu na tabbatar da dimokuraɗiyyar Nijeriya, zaman lafiya, da haɗin kai, waɗanda ke da muhimmanci ga martabar ƙasar a duniya.

 

Ministan ya kuma amince da The Guardian a matsayin babbar kafar yaɗa labarai, wanda tarihi ya danganta da gwagwarmayar dimokraɗiyyar Nijeriya da yaƙi da mulkin soja.

 

Ya buƙaci jaridar da ta ci gaba da jajircewarta kan manufofin dimokuraɗiyya da kuma yin watsi da duk wani tasiri da zai kawo barazana ga zaman lafiyar ƙasa.

 

Idris ya kuma bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta mayar da hankali ne kan kawo sauyi a fannin zamantakewa da tattalin arziƙin Nijeriya.

 

Da yake mayar da martani, Babban Jami’in The Guardian, Toke Ibru, ya tabbatar da aniyar ƙungiyar na inganta haɗin kai, zaman lafiya, da tsaro, tare da bayyana rawar da take takawa a matsayin babbar murya a ci gaban dimokuraɗiyyar Nijeriya.

 

Sauran waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Muƙaddashin Babban Sakatare na Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Misis Comfort Ajiboye, tare da wasu manyan jami’an gudanarwar The Guardian, da suka haɗa da Martins Oloja, Dr. Oluwafemi Adekoya, da Chuks. Nwanne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Fito Da Sabbin  Nau’in Kaji 2 Da Iri

Gwamnatin Tarayya Ta Fito Da Sabbin  Nau’in Kaji 2 Da Iri

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.