• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki

by Shehu Yahaya
8 months ago
in Labarai
0
Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da jihohin Arewacin kasar nan suke ci gaba da fuskantar matsalar rashin wutar lantarki, wadda ta shafi ma’aikatun gwamnati da masana’antu da kuma harkokin kasuwancin al’ummar yankin arewa, da aka kwashe kwanaki babu hasken wutar lantarki a yankin, wasu na ganin shiryayyen lamari ne na yi wa tattalin arzikin yankin zagon kasa.

Kungiyar dattawan arewa (NEF) ta bayyana cewa matsalar rashin wutar lantarki a arewa shiryayyen lamari ne, inda suka ce an yi haka ne domin yi wa tattalin arzikin arewa zagon kasa.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Horor Da Kasar Sin Take Tallafawa Ya Inganta Yaki Da Nakiyoyin Da Aka Binne A Somaliya

A zantawarsa da wakilinmu, mai magana da yawun kungiyar dattawan Arewa, Abdul-Azeez Suleiman, ya ce, “Ga dukkan mai hankali da kuma kishin Arewa ya san zagon kasa ne da nufin gurgunta yankin. Idan aka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa kafin rashin wutar, za a ga cewa rashin zaman lafiya ya hana noma, ya hana kiwo, ya hana karatu a Arewa. Yanzu ga wannan bakin duhu da aka jefa yankin a ciki.

“Masana sun tabbatar da cewa idan ana nufin gurgunta kasa ko yanki ko al’umma, matakin farko shi ne jefa ta cikin duhu. A yanzu a Arewa ba masana’antar da ke motsawa, ko nikan tuwo da garin kunu ya zama tashin hankali. Kun ga kenan duk matakai na gurgunta tattalin arziki da walwala da zaman lafiya duk sun bayyana. Sai dai fa Arewa ba ta da ikon zargin wani yanki game da wannan lamari.

Ya ci gaba da cewa, tun bayan mulkin su Sardauna Ahmadu Bello aka sami wadanda ba su damu da al’umma ba, sai kawunansu da iyalansu, suke ta sace dukiyoyi suna mayar da Arewa baya. Ya ce shugabannin Arewa su suka kashe duk ababen more rayuwa da Sardauna ya samar.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sai dai a nata bangaren, kungiyar gwamnonin Arewa ta nemi gwamnatin tarayya ta yi gaggawar shawo kan matsalar wutar lantarki da ake fama da ita a mafi yawan yankin.

Kungiyar ta yi kiran ne yayin taron da ta gudanar a fadar gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Gwamnonin tare da sarakunan gargajiya na shiyyar Arewacin kasar nan sun tattauna matsalolin da suka dabaibaye yankin. Sama da kwana takwas kenan da jefa yankunan Arewa maso yamma, da Arewa maso gabas, da wani bangare na Arewa ta tsakiyar cikin duhu sakamakon lalacewar babban tashar samar da wutar lantarki ta kasa.

Gwamna Inuwa ya kara da cewa, “Kungiyar na kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin da suka dace da su gaggauta shawo kan matsalar lantarki da mafi yawan jihohin arewaci ke ciki.

“Wannan lamari ba wai yana nuna girman hadarin rashin ababen more rayuwa ba ne kawai, yana kuma fito da bukatun gina wasu hanyoyin fadada samun wutar lantarki.”

A wata sanarwar da hukumar kula da wutar lantarki na Nijeriya (TCN) ta fitar, ta ce matsalar rashin wuta da ke addabar yankin Arewa za ta ci gaba saboda kalubalen tsaro da ke hana gyaran wasu muhimman layukan wutar.

Ya zuwa yanzu a Jihar Kaduna matsalar rashin wutar lantarki tana ci gaba da jefa al’umma cikin mawuyacin hali a yayin da harkokin kasuwanci suka yi tsaye cak.

Sai dai kuma matsalar ta kara yawaitar ‘yan ta’adda musamman masu kwacen wayar hannu a wuraren da ake yin cajin wayoyi.

Masu shagunan cajin waya sun shaida wa wakilinmu cewa a kullum suna zama cikin fargabar matasa masu zuwa da makamai suna kwace wayoyin mutane da suka kawo caji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaGwamnonin ArewaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

Related

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

2 hours ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

3 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

5 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

6 hours ago
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

13 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

16 hours ago
Next Post
Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba - Minista

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.