ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki

by Shehu Yahaya
2 years ago
Wutar Lantarki

A yayin da jihohin Arewacin kasar nan suke ci gaba da fuskantar matsalar rashin wutar lantarki, wadda ta shafi ma’aikatun gwamnati da masana’antu da kuma harkokin kasuwancin al’ummar yankin arewa, da aka kwashe kwanaki babu hasken wutar lantarki a yankin, wasu na ganin shiryayyen lamari ne na yi wa tattalin arzikin yankin zagon kasa.

Kungiyar dattawan arewa (NEF) ta bayyana cewa matsalar rashin wutar lantarki a arewa shiryayyen lamari ne, inda suka ce an yi haka ne domin yi wa tattalin arzikin arewa zagon kasa.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Horor Da Kasar Sin Take Tallafawa Ya Inganta Yaki Da Nakiyoyin Da Aka Binne A Somaliya

A zantawarsa da wakilinmu, mai magana da yawun kungiyar dattawan Arewa, Abdul-Azeez Suleiman, ya ce, “Ga dukkan mai hankali da kuma kishin Arewa ya san zagon kasa ne da nufin gurgunta yankin. Idan aka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa kafin rashin wutar, za a ga cewa rashin zaman lafiya ya hana noma, ya hana kiwo, ya hana karatu a Arewa. Yanzu ga wannan bakin duhu da aka jefa yankin a ciki.

ADVERTISEMENT

“Masana sun tabbatar da cewa idan ana nufin gurgunta kasa ko yanki ko al’umma, matakin farko shi ne jefa ta cikin duhu. A yanzu a Arewa ba masana’antar da ke motsawa, ko nikan tuwo da garin kunu ya zama tashin hankali. Kun ga kenan duk matakai na gurgunta tattalin arziki da walwala da zaman lafiya duk sun bayyana. Sai dai fa Arewa ba ta da ikon zargin wani yanki game da wannan lamari.

Ya ci gaba da cewa, tun bayan mulkin su Sardauna Ahmadu Bello aka sami wadanda ba su damu da al’umma ba, sai kawunansu da iyalansu, suke ta sace dukiyoyi suna mayar da Arewa baya. Ya ce shugabannin Arewa su suka kashe duk ababen more rayuwa da Sardauna ya samar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Sai dai a nata bangaren, kungiyar gwamnonin Arewa ta nemi gwamnatin tarayya ta yi gaggawar shawo kan matsalar wutar lantarki da ake fama da ita a mafi yawan yankin.

Kungiyar ta yi kiran ne yayin taron da ta gudanar a fadar gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Gwamnonin tare da sarakunan gargajiya na shiyyar Arewacin kasar nan sun tattauna matsalolin da suka dabaibaye yankin. Sama da kwana takwas kenan da jefa yankunan Arewa maso yamma, da Arewa maso gabas, da wani bangare na Arewa ta tsakiyar cikin duhu sakamakon lalacewar babban tashar samar da wutar lantarki ta kasa.

Gwamna Inuwa ya kara da cewa, “Kungiyar na kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin da suka dace da su gaggauta shawo kan matsalar lantarki da mafi yawan jihohin arewaci ke ciki.

“Wannan lamari ba wai yana nuna girman hadarin rashin ababen more rayuwa ba ne kawai, yana kuma fito da bukatun gina wasu hanyoyin fadada samun wutar lantarki.”

A wata sanarwar da hukumar kula da wutar lantarki na Nijeriya (TCN) ta fitar, ta ce matsalar rashin wuta da ke addabar yankin Arewa za ta ci gaba saboda kalubalen tsaro da ke hana gyaran wasu muhimman layukan wutar.

Ya zuwa yanzu a Jihar Kaduna matsalar rashin wutar lantarki tana ci gaba da jefa al’umma cikin mawuyacin hali a yayin da harkokin kasuwanci suka yi tsaye cak.

Sai dai kuma matsalar ta kara yawaitar ‘yan ta’adda musamman masu kwacen wayar hannu a wuraren da ake yin cajin wayoyi.

Masu shagunan cajin waya sun shaida wa wakilinmu cewa a kullum suna zama cikin fargabar matasa masu zuwa da makamai suna kwace wayoyin mutane da suka kawo caji.

Wutar Lantarki
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba - Minista

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.