ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki

by Shehu Yahaya
2 years ago
Wutar Lantarki

A yayin da jihohin Arewacin kasar nan suke ci gaba da fuskantar matsalar rashin wutar lantarki, wadda ta shafi ma’aikatun gwamnati da masana’antu da kuma harkokin kasuwancin al’ummar yankin arewa, da aka kwashe kwanaki babu hasken wutar lantarki a yankin, wasu na ganin shiryayyen lamari ne na yi wa tattalin arzikin yankin zagon kasa.

Kungiyar dattawan arewa (NEF) ta bayyana cewa matsalar rashin wutar lantarki a arewa shiryayyen lamari ne, inda suka ce an yi haka ne domin yi wa tattalin arzikin arewa zagon kasa.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Horor Da Kasar Sin Take Tallafawa Ya Inganta Yaki Da Nakiyoyin Da Aka Binne A Somaliya

A zantawarsa da wakilinmu, mai magana da yawun kungiyar dattawan Arewa, Abdul-Azeez Suleiman, ya ce, “Ga dukkan mai hankali da kuma kishin Arewa ya san zagon kasa ne da nufin gurgunta yankin. Idan aka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa kafin rashin wutar, za a ga cewa rashin zaman lafiya ya hana noma, ya hana kiwo, ya hana karatu a Arewa. Yanzu ga wannan bakin duhu da aka jefa yankin a ciki.

ADVERTISEMENT

“Masana sun tabbatar da cewa idan ana nufin gurgunta kasa ko yanki ko al’umma, matakin farko shi ne jefa ta cikin duhu. A yanzu a Arewa ba masana’antar da ke motsawa, ko nikan tuwo da garin kunu ya zama tashin hankali. Kun ga kenan duk matakai na gurgunta tattalin arziki da walwala da zaman lafiya duk sun bayyana. Sai dai fa Arewa ba ta da ikon zargin wani yanki game da wannan lamari.

Ya ci gaba da cewa, tun bayan mulkin su Sardauna Ahmadu Bello aka sami wadanda ba su damu da al’umma ba, sai kawunansu da iyalansu, suke ta sace dukiyoyi suna mayar da Arewa baya. Ya ce shugabannin Arewa su suka kashe duk ababen more rayuwa da Sardauna ya samar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sai dai a nata bangaren, kungiyar gwamnonin Arewa ta nemi gwamnatin tarayya ta yi gaggawar shawo kan matsalar wutar lantarki da ake fama da ita a mafi yawan yankin.

Kungiyar ta yi kiran ne yayin taron da ta gudanar a fadar gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Gwamnonin tare da sarakunan gargajiya na shiyyar Arewacin kasar nan sun tattauna matsalolin da suka dabaibaye yankin. Sama da kwana takwas kenan da jefa yankunan Arewa maso yamma, da Arewa maso gabas, da wani bangare na Arewa ta tsakiyar cikin duhu sakamakon lalacewar babban tashar samar da wutar lantarki ta kasa.

Gwamna Inuwa ya kara da cewa, “Kungiyar na kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin da suka dace da su gaggauta shawo kan matsalar lantarki da mafi yawan jihohin arewaci ke ciki.

“Wannan lamari ba wai yana nuna girman hadarin rashin ababen more rayuwa ba ne kawai, yana kuma fito da bukatun gina wasu hanyoyin fadada samun wutar lantarki.”

A wata sanarwar da hukumar kula da wutar lantarki na Nijeriya (TCN) ta fitar, ta ce matsalar rashin wuta da ke addabar yankin Arewa za ta ci gaba saboda kalubalen tsaro da ke hana gyaran wasu muhimman layukan wutar.

Ya zuwa yanzu a Jihar Kaduna matsalar rashin wutar lantarki tana ci gaba da jefa al’umma cikin mawuyacin hali a yayin da harkokin kasuwanci suka yi tsaye cak.

Sai dai kuma matsalar ta kara yawaitar ‘yan ta’adda musamman masu kwacen wayar hannu a wuraren da ake yin cajin wayoyi.

Masu shagunan cajin waya sun shaida wa wakilinmu cewa a kullum suna zama cikin fargabar matasa masu zuwa da makamai suna kwace wayoyin mutane da suka kawo caji.

Wutar Lantarki
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba - Minista

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.