• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

by Sulaiman
2 months ago
Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da aikin gyaran na’urar tiransimita mai gajeren zango (shortwave) ta gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) mai ƙarfin kilowat 250 TX2 a tashar da ke unguwar Lugbe a Abuja.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, wanda Babban Sakatare a ma’aikatar, Mista Ogbodo Chinasa Nnam ya wakilta, shi ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar wanda aka yi a ranar Talata a Abuja.

  • Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Idris ya bayyana wannan mataki a matsayin wani “muhimmin lokaci a tarihin Muryar Nijeriya, domin mun fara aikin farfaɗo da tasha mafi girma kuma mafi ƙarfi a nahiyar Afrika wadda yanzu ake sanya mata ingantattun na’urori na zamani da suka dace da fasahar zamani.”

 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Idris ya gode wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa hangen nesan sa da jajircewar sa wajen zamanantar da kayan aikin yaɗa labarai a Nijeriya.

 

A cewar sa: “Yayin da muke ɗaukar wannan babban mataki na ƙaddamar kwangilar gyara tiransimitar ‘shortwave’ ta Muryar Nijeriya mai ƙarfin kilowat 250, ya dace mu nuna ɗimbin godiyar mu ga Mai Girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa hangen nesa da jajircewar sa wajen farfaɗo da kuma zamanantar da kayan aikin yaɗa labarai na Muryar Nijeriya.”

 

Ya kuma tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa wannan aikin zai sauya yanayin yadda ake yaɗa labarai a ƙasar nan.

 

Ya ce: “Da zarar an kammala wannan aiki, na’urorin tiransimita na VON da aka farfaɗo da su gaba ɗaya za su sauya yanayin yaɗa shirye-shiryen rediyo na ƙasa, tare da sanya VON a matsayin gagarumar alama mai martaba a duniyar yaɗa labarai ta rediyo baki ɗaya.”

 

Ministan ya buƙaci kamfanin Confax Nigeria Limited da ke gudanar da kwangilar da ya tabbatar da inganci da kuma kammalawa a kan lokaci, inda ya ce: “Saboda haka ina kira ga ɗan kwangilar da ya tabbatar da ba wai kawai an kammala aikin a cikin lokacin da aka tsara ba, har ma a tabbatar da cewa an kiyaye mafi girman matakan inganci kuma hakan ya fito fili.”

 

Haka kuma ya umurci ma’aikatan da ke kula da na’urori a VON da su yi aiki da jajircewa da natsuwa wajen kula da wannan aikin.

 

Ya jaddada cewa ana sa ran gidan rediyon VON zai ci gaba da kiyaye manufar sa ta kasancewa gidan rediyo mai goyon bayan Nijeriya da Afrika baki ɗaya, tare da bayar da sahihan labarai na nasarorin da ke fitowa daga Nijeriya da nahiyar baki ɗaya.

 

A ƙarshe, Ministan ya ce: “Yanzu ina farin cikin ƙaddamar da kwangilar gyaran na’urar tiransimitar ‘shortwave’ ta Muryar Nijeriya mai ƙarfin kilowat 250.”

 

Shi dai VON, shi ne gidan rediyon da Gwamnatin Tarayya ta kafa domin bada labarai daga Nijeriya zuwa ƙasashen ƙetare, kwatankwacin gidan rediyon BBC da na Muryar Amurka.

 

An kafa shi a cikin 1961 a matsayin sashen labaran ƙetare na gidan rediyon NBC, wato wanda ya zama FRCN daga bisani. Firayim Minista na lokacin, Alhaji Sa Abubakar Tafawa Balewa, shi ne ya ƙaddamar da shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.