ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

by Sulaiman
10 months ago
Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da aikin gyaran na’urar tiransimita mai gajeren zango (shortwave) ta gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) mai ƙarfin kilowat 250 TX2 a tashar da ke unguwar Lugbe a Abuja.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, wanda Babban Sakatare a ma’aikatar, Mista Ogbodo Chinasa Nnam ya wakilta, shi ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar wanda aka yi a ranar Talata a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Idris ya bayyana wannan mataki a matsayin wani “muhimmin lokaci a tarihin Muryar Nijeriya, domin mun fara aikin farfaɗo da tasha mafi girma kuma mafi ƙarfi a nahiyar Afrika wadda yanzu ake sanya mata ingantattun na’urori na zamani da suka dace da fasahar zamani.”

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Idris ya gode wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa hangen nesan sa da jajircewar sa wajen zamanantar da kayan aikin yaɗa labarai a Nijeriya.

 

A cewar sa: “Yayin da muke ɗaukar wannan babban mataki na ƙaddamar kwangilar gyara tiransimitar ‘shortwave’ ta Muryar Nijeriya mai ƙarfin kilowat 250, ya dace mu nuna ɗimbin godiyar mu ga Mai Girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa hangen nesa da jajircewar sa wajen farfaɗo da kuma zamanantar da kayan aikin yaɗa labarai na Muryar Nijeriya.”

 

Ya kuma tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa wannan aikin zai sauya yanayin yadda ake yaɗa labarai a ƙasar nan.

 

Ya ce: “Da zarar an kammala wannan aiki, na’urorin tiransimita na VON da aka farfaɗo da su gaba ɗaya za su sauya yanayin yaɗa shirye-shiryen rediyo na ƙasa, tare da sanya VON a matsayin gagarumar alama mai martaba a duniyar yaɗa labarai ta rediyo baki ɗaya.”

 

Ministan ya buƙaci kamfanin Confax Nigeria Limited da ke gudanar da kwangilar da ya tabbatar da inganci da kuma kammalawa a kan lokaci, inda ya ce: “Saboda haka ina kira ga ɗan kwangilar da ya tabbatar da ba wai kawai an kammala aikin a cikin lokacin da aka tsara ba, har ma a tabbatar da cewa an kiyaye mafi girman matakan inganci kuma hakan ya fito fili.”

 

Haka kuma ya umurci ma’aikatan da ke kula da na’urori a VON da su yi aiki da jajircewa da natsuwa wajen kula da wannan aikin.

 

Ya jaddada cewa ana sa ran gidan rediyon VON zai ci gaba da kiyaye manufar sa ta kasancewa gidan rediyo mai goyon bayan Nijeriya da Afrika baki ɗaya, tare da bayar da sahihan labarai na nasarorin da ke fitowa daga Nijeriya da nahiyar baki ɗaya.

 

A ƙarshe, Ministan ya ce: “Yanzu ina farin cikin ƙaddamar da kwangilar gyaran na’urar tiransimitar ‘shortwave’ ta Muryar Nijeriya mai ƙarfin kilowat 250.”

 

Shi dai VON, shi ne gidan rediyon da Gwamnatin Tarayya ta kafa domin bada labarai daga Nijeriya zuwa ƙasashen ƙetare, kwatankwacin gidan rediyon BBC da na Muryar Amurka.

 

An kafa shi a cikin 1961 a matsayin sashen labaran ƙetare na gidan rediyon NBC, wato wanda ya zama FRCN daga bisani. Firayim Minista na lokacin, Alhaji Sa Abubakar Tafawa Balewa, shi ne ya ƙaddamar da shi.

Rediyon Muryar Nijeriya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Sulaiman
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Sulaiman
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sulaiman
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

MASU ALAKA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
Labarai

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Next Post
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.