• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Umarci Mayar Da Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Shafa A Suleja Zuwa Manyan Asibitoci

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamnati Ta Umarci Mayar Da Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Shafa A Suleja Zuwa Manyan Asibitoci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin gaggawa na tura mutanen da suka jikkata a hatsarin fashewar tankar man fetur da ya faru a Suleja, Jihar Neja, daga Asibitin Suleja zuwa manyan asibitoci domin samun ingantacciyar kulawar lafiya cikin sauri.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyara da ya kai Suleja a ranar Lahadi.

  • Tinubu Ya Himmatu Wajen Kammala Titin Abuja Zuwa Kano Cikin Watanni 14 – Minista
  • TikTok Ya Dawo Aiki A Amurka Bayan Matakin Da Trump Ya Ɗauka 

Idris ya jagoranci wata tawaga daga Gwamnatin Tarayya, ciki har da Ministan Harkokin Jinƙai da Rage Talauci, Dr. Nentawe Yilwatda, domin tantance halin da ake ciki da kuma miƙa ta’aziyyarsu ga Gwamnatin Jihar Neja da mazauna yankin bisa hatsarin da ya faru a Dikko Junction.

 

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

“Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana cikin matuƙar jimami kan wannan mummunan al’amari. Ya umurce mu da mu zo nan don ganin halin da ake ciki. Mun zagaya ɗakin masu jinya, kuma mun ga waɗanda ke cikin mummunan hali. Muna nan ana duba su, amma abin takaici, ɗaya daga cikinsu ya rasu. Wannan shi ne mutum na takwas da ya rasu sakamakon wannan hatsari. Gwamnatin Tarayya za ta tabbatar da cewa an yi gaggawar tura waɗannan mutanen da suka jikkata zuwa manyan asibitoci,” inji Idris.

 

Ministan ya yaba da gaggawar Gwamnatin Jihar Neja wajen bayar da taimakon gaggawa ga waɗanda suka jikkata.

 

Yayin da yake bayyana damuwarsa kan yawaitar fashewar tankar man fetur a ƙasar, inda mutane sama da 265 suka rasa rayukansu a cikin watanni biyar, Idris ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Tinubu ya kafa kwamiti domin bincikar musabbabin faruwar waɗannan al’amura da kuma samar da mafita don hana faruwar hakan a gaba.

 

“Shugaban ƙasa yana cikin damuwa sosai game da abin da ya faru. Ya kafa kwamitin bincike na musamman don gano musabbabin waɗannan abubuwan. A cikin watanni biyar da suka gabata, mun fuskanci manyan haɗura huɗu: ɗaya tsakanin Ibadan da Ife, wani a Agaie, Jihar Neja, inda mutane 48 suka rasa rayukansu, wani kuma a Jihar Jigawa inda mutane 144 suka mutu, sannan wannan a Suleja inda kusan mutane 80 suka mutu. Idan aka haɗa yawan waɗanda suka rasa rayukansu, sama da mutane 265 ne suka mutu a irin waɗannan haɗurra.

 

“Kwamitin da aka kafa, wanda ya ƙunshi manyan ma’aikatu da hukumomi kamar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, NEMA, FRSC, NUPRC, da NARTO, zai binciki musabbabin haɗurran tare da bayar da shawarwari don hana sake faruwar su,” inji Idris.

 

Ministan ya ce, a bisa umarnin da Shugaban Ƙasa ya bayar kwanan nan, Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) za ta ƙara himma wajen wayar da kan jama’a kan haɗarin kwasan man fetur daga tankokin mai da suka yi hatsari domin hana aukuwar irin waɗannan al’amura nan gaba. Ya yi tir da wannan ɗabi’a, yana mai bayyana ta a matsayin abin da ba za a yarda da shi ba.

 

Tawagar ta fara kai ziyara ta jaje ga Sarkin Suleja, Alhaji Auwal Ibrahim, sannan ta ziyarci waɗanda suka jikkata a Asibitin Suleja da wurin da haɗarin ya faru.

 

Sauran waɗanda suka kasance a tawagar har da Daraktocin Janar na Gidan Talabijin na Nijeriya (NTA), Abdulhamid Dembos; Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace; da Rediyon Tarayya na Nijeriya (FRCN), Mohammed Bulama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sace Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki 18 A Cikin Kwanaki 6 – TCN

Next Post

Bidiyon Rashin Ɗa’a: Hukumar Tace Fina-finai Ta Dakatar Da Soja-boy Daga Shiga Duk Wata Harka Ta Kannywood

Related

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

2 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

12 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

13 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

17 hours ago
Next Post
Bidiyon Rashin Ɗa’a: Hukumar Tace Fina-finai Ta Dakatar Da Soja-boy Daga Shiga Duk Wata Harka Ta Kannywood

Bidiyon Rashin Ɗa'a: Hukumar Tace Fina-finai Ta Dakatar Da Soja-boy Daga Shiga Duk Wata Harka Ta Kannywood

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.