• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Tarayya Ta Dakatar Da Shirin N-Power

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnati Tarayya Ta Dakatar Da Shirin N-Power
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirin N-Power har illa-masha-Allah. 

Matakin na zuwa ne bisa wasu abubuwan da aka gano game da shirin wanda ba daidai ba.

  • Masu Laifi 222 Sun Mika Wuya, An Cafke 98 A Kano
  • Mutane Miliyan 826 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Ranaikun Hutu Na Kasar Sin

A cewar gwamnati, daukan matakin dakatarwar na zuwa ne bisa gano wasu kura-kurai da suke makale a shirin, kuma, tunin aka kaddamar da bincike kan yadda aka sarrafa kudaden da aka fitar tun lokacin fara aiwatar da shirin.

Ministar kula da harkokin jin-kai da yaki da fatara, Betta Edu, ita ce ta sanar da hakan yayin da take magana ta cikin wani shirin labaran talabijin din ‘TVC’ a ranar Asabar, ta yi ikirarin cewa wasu da suke cin gajiyar shirin ba su zuwa wuraren da aka turasu aiki, amma har yanzu su na tsamamanin a biyasu alawus-alawus na wata-wata.

Edu ta kara da cewa wasu da suke cikin shirin sun kammala cin moriya tun 2022 amma har yanzu suna cikin jerin wadanda ake biya.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

“Dole ne mu waiwaya baya mu duba shirin N-Power kuma mun gano akwai kura-kurai don haka mun dakatar da shirin a yanzu har zuwa lokacin da za a kammala gudanar da cikakken bincike kan yadda aka sarrafa kudaden shirin N-Power.”

Ta ce, dole su gano mutum nawa ne suke cikin shirin a halin yanzu da kuma bashin da ke tattare da shi tare da gano mutum nawa ne bashin ya shafa, a cewarta gabaki daya suna son sauya fasalin tarin N-Power da ma fadada shi.

“Abubuwa da dama su na kan faruwa. Mun samu mutanen da ya dace su fita daga cikin shirin tun shekarar da ta gabata amma har yanzu suna kan ikirarin cewa suna koyarwa.

“Wasu lokutan idan muka tuntubi makarantu ko wuraren da aka turasu aiki sai a tarar ba su zuwa ba su nan gaba daya. Ba su aikin amma su na ta ikirarin cewa suna bin bashin alawus na wata tawas ko wata tara. Kusan kaso 80 cikin 100 ba su aikin amma suna ta neman a biyasu albashi,” ta shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Aikin Raya Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ya Samar Da Sabbin Damammaki Ga Duniya A Cewar Kusoshin Siyasa Na Kasashe Da Dama

Next Post

“Makon Zinare” Ya Kore Surutan Tabarbarewar Tattalin Arzikin Kasar Sin 

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

4 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

6 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

10 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

11 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

14 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

1 day ago
Next Post
Makon Zinare

“Makon Zinare” Ya Kore Surutan Tabarbarewar Tattalin Arzikin Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.