• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa’azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama’a

by Sadiq
3 years ago
Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi ta ce ba za ta lamunci kalaman tunzura jama’a daga duk wani mai wa’azi a jihar ba.

Sakataren gwamnatin jihar, Mista Ibrahim Kashim ne ya yi wannan gargadin yayin da yake zantawa da manema labarai sakamakon taron kwamitin tsaro na jihar, a ranar Litinin a Bauchi.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Kasar Sin Ba Ita Ce Tushen Saka Wa Kasashen Afirka Tarkon Bashi Ba
  • An Kama ‘Yansanda Biyar Da Dan Kasuwa A Filato

A cewarsa, gwamnati za ta tunkari duk wani mai wa’azi da ya yi kalaman da zai iya haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin jama’a.

“Kamar yadda kuka sani, muna fitowa ne daga cikin mawuyacin halin da ake ciki na yakin neman zabe kuma abubuwa da dama sun faru bayan zaben da ke bukatar tsauraran matakan tsaro.

“An yi ta hayaniya wasu kuma kan batutuwan da suka shafi wa’azi da fahimtar mahallin wa’azi da kuma abin da ya haifar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

“Mun damu saboda ba batun Akida ba ne, ba batun siyasa ba ne kawai batun tunzura maganganun da za su haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin al’ummarmu.

“Mun gana, mun tattauna kuma mun yanke shawarar cewa Bauchi wuri ne mai matukar zaman lafiya, kuma za mu yi duk abin da za mu iya don ganin an zauna lafiya.

“Ba za mu bari wani abu ko maganganun wani ya kawo cikas ga zaman lafiyar da muke samu a jihar ba,” in ji shi.

Kashim wanda kuma shi ne Shugaban Kwamitin Tsaro, ya kara da cewa gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya kara da cewa “Ba za mu kyale wani daga yanzu ya ci mutuncin wani ko cin mutuncin imanin wani ko wasu mutane dangane da imaninsu ba,” in ji shi.

Shi ma da yake jawabi, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aminu Alhassan, ya bayyana cewa ana kokarin dakile ayyukan da za su iya kawo cikas ga zaman lafiya a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
Manyan Labarai

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Next Post
An Haramta Wa Limamai Karanta Alkur’ani Daga Waya A lokutan Sallolin Dare A Kuwait

An Haramta Wa Limamai Karanta Alkur’ani Daga Waya A lokutan Sallolin Dare A Kuwait

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.