• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

by Sadiq
2 years ago
Bauchi

Gwamnatin jihar Bauchi ta soke nadin Mista Aminu Umar, shugaban kungiyar riko na kungiyar kwallon kafa ta WIkki Tourists Football Club (FC), ba tare da bata lokaci ba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan matasa da wasanni na jihar, Muhammed Salis Gamawa, kuma ya bayyana wa manema labarai ranar Laraba a Bauchi.

  • Ina Son Ci Gaba Da Zama Kyaftin Din Ingila Har Zuwa 2028 – Harry Kane
  • NIS Za Ta Sayo Jirage Masu Sarrafa Kansu Don Aikin Sintiri A Iyakokin Nijeriya

“Ina sanar da ku shawarar da muka yanke na dakatar da aikinku na rikon kwarya na kungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourists, wanda zai fara aiki nan da nan (yau).

“Nadin da aka yi muku a matsayin shugaban rikon kwarya don tafiyar da kungiyar ta hanyar da ta dace.

“Duk da haka, mun lura da jerin ayyuka da suka saba wa ka’idojin da aka bayar don gudanar da kungiyar yadda ya dace.

LABARAI MASU NASABA

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta

“An aikata abubuwan da suka haifar da cikas ga rikon amana da ingantaccen shugabanci da muke sa rai a kungiyar.

“Saboda haka, ba mu da wani zabi illa mu soke shugabancinku na wucin gadi,” in ji kwamishina.

Kwamishinan ya ce gwamnatin jihar ta yaba da kokarin da shugabannin suka yi a kungiyar tare da jajircewa wajen samun nasarar kungiyar.

“Duk da haka, dole ne mu kiyaye ka’idojin shugabanci nagari, kula da harkokin kudi da kuma bin ka’idojin da aka kafa.

“Mun yi imanin cewa wannan shawarar za ta zama wata dama a gare ku da kungiyar don sake tantancewa da ci gaba ta hanyar da ta dace da gaskiya da kwarewa,” in ji shi.

Sai dai Salis ya yi wa Umar fatan alheri a rayuwarsa ta gaba, tare da fatan zai ci gaba da bayar da gudunmawa ga harkokin wasanni.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
Tsaro

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

October 11, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Tsaro

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta

October 11, 2025
Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano
Labarai

Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano

October 11, 2025
Next Post
Tinubu Ya Nada Olukoyede A Matsayin Sabon Shugaban EFCC

Tinubu Ya Nada Olukoyede A Matsayin Sabon Shugaban EFCC

LABARAI MASU NASABA

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

October 11, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta

October 11, 2025
Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano

Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.