• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Gombe Zata Fadada Hanyoyin Ture, Bakasi Zuwa Gelengu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Gombe Zata Fadada Hanyoyin Ture, Bakasi Zuwa Gelengu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Gombe ta cimma matsayar fadada wasu muhimman hanyoyi biyu na Ture zuwa Dogon Ruwa zuwa Gelengu, dana Bakasi zuwa Gelengu, wadanda gwamnatin baya ta fara.

Kwamishinan Ayyuka da Sufuri na jihar Injiniya Abubakar Musa Bappa ne ya bayyana hakan ranar Larabar yayin wani taron manema labarai kan sakamakon zaman majalisar zartarwa ta jiha karo na 23 daa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya jagoranta a zauren majalisar zartaswa ta jiha dake gidan gwamnati.

  • Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 

Ya ce, “Hanyar Ture zuwa Dogon Ruwa mai tsawon kilomita 23, gwamnatin da ta gabata ce ta bayar da aikin ta a 2013 kan kudi Naira biliyan 2 da miliyan 600 amma ta yi watsi da ita saboda rashin biyan ‘yan kwangila, amma gwamnatin Muhammadu Inuwa Yahaya ta ga dacewar karisa aikin tare da tsawaita hanyar da kimanin kilomita 19 zuwa Gelengu dake karamar hukumar Balanga bisa karin kudi Naira biliyan 2 da miliyan 900”.

Kwamishinan ya ce shi ma aikin hanyar Bakasi zuwa Talasse da aka yi watsi da ita mai tsawon kusan kilomita 10 wacce ta hade kauyuka da dama za a kammala ta kan kudi Naira biliyan 2 da miliyan 600. Ya ce “Idan aka kammala aikin, hanyar zata bunkasa harkokin noma da tattalin arziki da zamantakewar al’ummomin wannan yankin”.

Ya kara da cewa majalisar ta kuma amince da daga darajar aikin titin Dukku zuwa Jamari mai tsawon kimanin kilomita 6 a karamar jukumar Dukku kan kudi Naira miliyan 557.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Injiniya Bappa ya ce ma’aikatar ta ziyarci wasu hanyoyi da dama da suka zagwanye sakamakon ruwan sama, inda wasu su ma suka yanke, yana mai cewa “Gwamnatin jihar ta tantance yanayin lalacewar hanyoyin kuma ta fara daukan matakan gyara”.

A nasa bangaren, Kwamishinan Kudi da Bunkasa Tattalin Arziki na Jihar Muhammad Gambo Magaji, ya ce majalisar ta amince da tsarin kashe kudaden na matsakaicin zango daga 2023 zuwa 2025 don mikawa Majalisar Dokokin Jiha tayi dubi tare da amincewa da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Amince Da Bayar Da Belin Wanda Ya Yi Garkuwa Da Yayarsa A Zariya

Next Post

Matukar Nijeriya Ba Ta Sanya Idanu Kan Kudaden Shigarta Ba Akwai Matsala —Bankin Duniya

Related

Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

10 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

12 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

16 hours ago
Zaman lafiya
Labarai

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

18 hours ago
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
Manyan Labarai

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

19 hours ago
Next Post
Matukar Nijeriya Ba Ta Sanya Idanu Kan Kudaden Shigarta Ba Akwai Matsala —Bankin Duniya

Matukar Nijeriya Ba Ta Sanya Idanu Kan Kudaden Shigarta Ba Akwai Matsala —Bankin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.