• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Bada Tabbacin Inganta Daidaiton Jinsi Da Karfafa Mata.

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada tabbacin kudirinta na inganta daidaiton jinsi da kuma tafiya da Mata a dukkan shirye-shiryenta na kawo cigaba.

Mataimakiyar gwamnan jihar, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe ce ta bayyana haka a wani taro da aka shirya kan nauyin da ya rataya akan jjinsi mabanbanta, wanda kungiyar Mata ta Majalisar Dinkin Duniya tare da hadin guiwar Bankin Raya Afirka (AfDB) da Gidauniyar Zamani suka shirya a Kaduna.

  • Dalilin Da Ya Sa Muka Dauki Matasa 7,000 Aikin ‘Yanbanga – Gwamnatin Kaduna

Dakta Balarabe ta bayyana cewa, gwamnatin Sanata Uba Sani ta yi imanin cewa, baiwa Mata dama ba wai kawai ya dace ba ne, babbar dabara ce ta habbaka tattalin arzikin jihar wanda za su iya bunkasa ci gaba, rage talauci, da inganta hadin kan al’umma.

A cewar Dokta Hadiza Balarabe, Nijeriya ta zama cikakkiyar kasa, dole ne ta tafi da Mata don su ne rabin al’ummar kasar kuma a daina tauye su ta hanyar cin zarafinsu.

Ta nanata cewce, Mata suna fuskantar tauyewa a zamantakewa da ra’ayoyin al’adu da ke lalata karfin tattalin arzikinsu da jagoranci, kamar wariyar jinsi, tsangwama, da kuma son zuciya.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Kaduna

Mataimakiyar Gwamnan, ta kara da cewa, al’amuran da suka shafi mata a koyaushe abin farin ciki ne a zuciyarta inda ta ce, “a matsayina na Mace kuma Uwa, kullum ina fuskantar wadannan kalubale. Mata ba su da cikakkiyar damar samun jarin kasuwanci, fasaha, kwarewa, da bayanai kamar yadda Maza ke samu”.

A nata jawabin, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya kan harkokin Mata a Nijeriya da kungiyar ECOWAS, Beatrice Eyong, ta ce kashi daya ne kacal na harkar saye da sayarwa a Nijeriya ke zuwa ga bangaren Mata ‘yan kasuwa, don haka akwai bukatar shirya taro don horaswa ta yadda za a lalubo mafita.

Kaduna

A nata jawabin, Shugabar Gidauniyar Zamani, Misis Talatu P. Zamani-Henry ta bayyana cewa, an shirya taron ne domin shawo kan kalubalen daidaiton jinsi kan samar da damar shigo da kayayyaki a jihar Kaduna da kewayenta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daidaiton jinsiKadunaKungiyoyin mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Sin Ta Sanya Wasu Kamfanonin Tsaron Amurka Biyu Takunkumi

Related

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato
Tsaro

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

23 minutes ago
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

1 hour ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

3 hours ago
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
Labarai

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

4 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

5 hours ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
Labarai

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

5 hours ago
Next Post
Sin

Sin Ta Sanya Wasu Kamfanonin Tsaron Amurka Biyu Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

May 11, 2025
Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.