• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da biyan sama da naira biliyan 16 na hakkokin ritaya da wasu alawus ga tsoffin kansiloli da sauran masu rike da mukaman siyasa a kananan hukumomi 44 na jihar. Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya jagoranci bikin kaddamarwar a ranar Laraba, inda ya bayyana cewa wannan biyan hakkoki ba alfarma ba ce, sai dai hakkinsu ne bisa adalci da godiya ga ayyukan da suka yi.

Gwamna Yusuf ya bayyana cewa wadanda suka ci gajiyar wannan tsari sun hada da kansiloli, mataimakan shugabannin karamar hukuma, shugabannin karamar hukuma, kwamishinonin gudanarwa da kuma mashawarta na musamman da suka yi aiki daga shekarar 2014 zuwa 2024. Ya ce gwamnatin NNPP ba za ta ci gaba da irin rashin adalcin da gwamnatin baya ta yi musu ba, inda ta ki biyansu hakkokinsu na ritaya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

An raba biyan kudi zuwa matakai uku:

  • Sashi na A (2014–2017): Naira biliyan 1.8 ga mutane 903 (za a biya nan take)
  • Sashi na B (2018–2020): Naira biliyan 5.6 ga mutane 1,198 (za a biya daga Mayu zuwa Yuli 2025)
  • Sashi na C (2021–2024): Naira biliyan 8.2 ga mutane 1,371 (za a biya daga Agusta zuwa Nuwamba 2025)

Haka kuma, an ware naira biliyan 1.27 don biyan kudin gidaje da kayan daki ga masu rike da mukaman siyasa na yanzu a kananan hukumomi.

Gwamna Yusuf ya kara da cewa wannan mataki alamar girmamawa ne ga masu yi wa kasa hidima, tabbatar da alkawari da kuma nuna amana a shugabanci. Ya yaba da kokarin dukkan bangarorin da suka taimaka wajen tabbatar da sahihancin wadanda suka cancanci biyan da kuma aiwatar da tsarin yadda ya kamata. Ya kuma roki hadin kai da goyon bayan al’umma wajen gina Jihar Kano mai cike da adalci da ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Next Post

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

Related

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

6 minutes ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

10 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

11 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

13 hours ago
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba
Manyan Labarai

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

14 hours ago
Next Post
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

June 20, 2025
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

June 20, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.