Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da biyan sama da naira biliyan 16 na hakkokin ritaya da wasu alawus ga tsoffin kansiloli da sauran masu rike da mukaman siyasa a kananan hukumomi 44 na jihar. Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya jagoranci bikin kaddamarwar a ranar Laraba, inda ya bayyana cewa wannan biyan hakkoki ba alfarma ba ce, sai dai hakkinsu ne bisa adalci da godiya ga ayyukan da suka yi.
Gwamna Yusuf ya bayyana cewa wadanda suka ci gajiyar wannan tsari sun hada da kansiloli, mataimakan shugabannin karamar hukuma, shugabannin karamar hukuma, kwamishinonin gudanarwa da kuma mashawarta na musamman da suka yi aiki daga shekarar 2014 zuwa 2024. Ya ce gwamnatin NNPP ba za ta ci gaba da irin rashin adalcin da gwamnatin baya ta yi musu ba, inda ta ki biyansu hakkokinsu na ritaya.
- ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano
- Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
An raba biyan kudi zuwa matakai uku:
- Sashi na A (2014–2017): Naira biliyan 1.8 ga mutane 903 (za a biya nan take)
- Sashi na B (2018–2020): Naira biliyan 5.6 ga mutane 1,198 (za a biya daga Mayu zuwa Yuli 2025)
- Sashi na C (2021–2024): Naira biliyan 8.2 ga mutane 1,371 (za a biya daga Agusta zuwa Nuwamba 2025)
Haka kuma, an ware naira biliyan 1.27 don biyan kudin gidaje da kayan daki ga masu rike da mukaman siyasa na yanzu a kananan hukumomi.
Gwamna Yusuf ya kara da cewa wannan mataki alamar girmamawa ne ga masu yi wa kasa hidima, tabbatar da alkawari da kuma nuna amana a shugabanci. Ya yaba da kokarin dukkan bangarorin da suka taimaka wajen tabbatar da sahihancin wadanda suka cancanci biyan da kuma aiwatar da tsarin yadda ya kamata. Ya kuma roki hadin kai da goyon bayan al’umma wajen gina Jihar Kano mai cike da adalci da ci gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp