• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Za Ta Biya Wadanda Ta Yi Wa Rusau Diyyar N3bn

by Sadiq
2 years ago
Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta amince ta biya diyyar Naira biliyan uku ga kungiyar masu shagunan Masallacin Idi saboda rusa musu kadarorin da aka yi musu ba bisa ka’ida ba.

An cimma yarjejeniyar ne ta wata takardar neman sasanci a ranar 12 ga watan Disamba tare da gabatar da kara a ranar 13 ga watan Disamba ta hannun lauyoyi ga masu shari’a, Inyang Ekwo na wata babbar kotun tarayya da ke Abuja.

  • Yadda Matashi Ya Yi Yunƙurin Hallaka Matarsa Don Ya Samu Damar Sace Mata Talabijin
  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 13, Sun Ceto Mutane 268 A Katsina

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya ya bayyana hakan ne biyo bayan rushe shagunan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi.

Masu shagunan sun kai karar gwamnatin jihar da hukumar tsare-tsare ta Jihar Kano (KNUPDA); babban lauyan gwamnati, ‘yansanda; Mataimakin Sufeto Janar na ‘yansanda shiyya 1 da ke Kano; Kwamishinan ‘yansanda, Kano; Kwamandan Hukumar Tsaro da Tsaron Farar Hula (NSCDC) kara.

Mai shari’a Samuel Amobeda, a ranar 29 ga watan Satumba a wani hukunci da ya yanke, ya umuaci gwamnatin jihar ta biya ‘yan kasuwar naira biliyan 30 a matsayin diyyar Naira biliyan 250 da ‘yan kasuwar ke nema, kan rushe musu kadarorin da aka yi.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Amma sakamakon kin bin umarnin kotun Kano da gwamnatin jihar ta yi, ‘yan kasuwar sun shigar da karar a gaban mai shari’a Ekwo, inda suka nemi a tilasta wa gwamnatin biyan su.

Hakan ne ya sa kotu bada umarnin rufe asusun ajiyar bankin gwamnatin jihar kan kin bin umarninta.

Sai dai kuma da aka ci gaba da sauraren karar a ranar Alhamis, Lauyan masu kara, Dokta N. A. Ayagi, ya shaida wa kotun cewa bangarorin biyu sun cimma matsayar biyan kudin.

Daga nan sai Ayagi ya bukaci kotun da ta amince da shirin sansancin cikin masalaha.

Har ila yau, lauyan wadanda ake kara, Affis Matanmi, bai ce komai kan hakan ba, don haka mai shari’a Ekwo ya yanke hukuncin kamar yadda bangarorin biyu suka aminta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Next Post
Xi Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Takwaransa Na Kenya Kan Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Kenya

Xi Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Takwaransa Na Kenya Kan Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Kenya

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.