• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Matawalle Ce Ta Rura Wutar Ta’addanci A Arewa – Turji

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Matawalle Ce Ta Rura Wutar Ta’addanci A Arewa – Turji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, da ke ta’addanci a arewacin Nijeriya, ya zargi karamin ministan tsaro kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da rashin kula da lamarin sulhu da ‘yan bindiga yadda ya kamata a lokacin da yake gwamnan jihar.

 

A lokacin da yake gwamna, Matawalle ya kaddamar da shirin yin afuwa ga ‘yan bindiga inda ya bayyana tattaunawa a matsayin mafi kyawun zabi na magance ta’addancin ‘yan bindiga.

  • Jihar Kano Na Shirin Gudanar Da Zaben Ƙananan Hukumomi – Gwamna Abba
  • Shugaba Tinubu Ya Mika Sakon Ta’aziyya ga Kasar Vietnam Kan Rasuwar Nguyễn Phú Trọng

Sai dai kuma daga baya ya janye afuwar, yana mai cewa ‘yan bindigar sun gaza rungumar shirin zaman lafiyar da gwamnatinsa ta yi musu.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

A cikin wani faifan bidiyo da aka saki a shafukan sada zumunta kuma Daily Trust ta nakalto, Turji ya alakanta karuwar ta’addanci a Zamfara da sauran jihohin Arewa maso Yamma kan manufofin da Matawalle ya tsara a lokacin da yake gwamna.

 

“Duk mutumin da ke zaune a Shinkafi, Zurmi, da Isa (Jihar Sokoto) ba zai iya musanta wannan ikirari ba. Akwai wasu gungun ‘yan bindiga da suka zama ‘yan lelen tsohon gwamnan. Na kore su daga Shinkafi, na kashe shugabansu, Dudu, domin samun dawwamammen zaman lafiya a Shinkafi. Kungiyar na da makamai 200, amma daga baya gwamnan ya karbe su (Yaran Dudu) a gidan gwamnati.

 

“Kuma gwamnati ta gaza nemansu (Yaran Dudu) da su mika makamansu. Sannan akwai Wata kungiya da Bashari Maniya ke jagoranta tana da bindigogi sama da 300.”

 

Turji ya yi ikirarin cewa, ya kwace bindigu 30 daga hannun sansanin ‘yan bindigar da ke karkashin jagorancin Bashari Maniya, kuma kungiyar ba ta taba mika makamanta ga gwamnati ba.

 

A cikin faifan bidiyon, Turji ya kuma yi zargin cewa, wasu shugabannin kungiyoyin ‘yan bindiga da ke cikin yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin Matawalle ta kaddamar sun koma Sokoto da zama bayan sun bai wa yaransu makamai domin ci gaba da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

 

“Ali yaro ne ga Kabiru Maniya, kuma shi ne ke da alhakin kai hare-hare a yankin Tangaza. Bashiri da Kabiru duk suna zaune ne a cikin babban birnin Sokoto, suna jin dadin rayuwarsu. Akwai Wani Buhari, shi ma yana cikin garin Sokoto yana jin dadin rayuwarsa.

 

“Makonni uku da suka wuce, an kama wani kanin Buhari da bindigogi a cikin babban birnin Sokoto. Babu mai musanta wannan. Zan iya fitowa da hujjojin bidiyo wanda ke nuna yadda Kabiru Maniya ke harba manyan bindigogi.

 

“Abin tambaya a yanzu shi ne, ina bindigoginsu bayan da suka ce sun rungumi zaman lafiya sun zauna a garin Sokoto?

 

Ya dace gwamnati ta bayyana wa ’yan Nijeriya wanda ke da alhakin kashe jama’a. Su daina zargin Bello Turji da kashe-kashe da garkuwa da mutane.

 

“Mutanen da ake garkuwa da su a cikin babban birnin Sokoto aka kai su bayan Achida da Goronyo, wa ke da alhakin yin garkuwa da su? Har yanzu Bello Turji ne ? Wanda yake zaune lafiya a Shinkafi?

 

Kokarin jin ta bakin Matawalle domin jin ta bakinsa ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

 

Kiraye-kiraye da yawa da aka yi wa Henshaw Ogubike, mai magana da yawun ma’aikatar tsaro, ya ci tura.

 

Ogbuike, ya aika da sakon tes, inda ya nemi wakilin Daily trust ya yi masa bayanin kiran ta hanyar rubutu (tes) amma bai mayar da martani ga sakon da aka aika masa ba har zuwa lokacin rubuta wannan rahoton.

 

A baya dai Matawalle ya musanta alaka da ‘yan bindigar, ya kuma kara da cewa, gwamnatinsa ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta magance matsalolin tsaro a Zamfara a lokacin da yake kan mulki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan bindigar ZamfaraTabarbarewar tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarkin Katsina Ya Jinjinawa Tinubu Kan Aikin Titin Maraba Zuwa Katsina

Next Post

An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

3 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

8 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

10 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

13 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

17 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

18 hours ago
Next Post
An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.