• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Matawalle Ce Ta Rura Wutar Ta’addanci A Arewa – Turji

by Sulaiman
12 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Matawalle Ce Ta Rura Wutar Ta’addanci A Arewa – Turji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, da ke ta’addanci a arewacin Nijeriya, ya zargi karamin ministan tsaro kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da rashin kula da lamarin sulhu da ‘yan bindiga yadda ya kamata a lokacin da yake gwamnan jihar.

 

A lokacin da yake gwamna, Matawalle ya kaddamar da shirin yin afuwa ga ‘yan bindiga inda ya bayyana tattaunawa a matsayin mafi kyawun zabi na magance ta’addancin ‘yan bindiga.

  • Jihar Kano Na Shirin Gudanar Da Zaben Ƙananan Hukumomi – Gwamna Abba
  • Shugaba Tinubu Ya Mika Sakon Ta’aziyya ga Kasar Vietnam Kan Rasuwar Nguyễn Phú Trọng

Sai dai kuma daga baya ya janye afuwar, yana mai cewa ‘yan bindigar sun gaza rungumar shirin zaman lafiyar da gwamnatinsa ta yi musu.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

A cikin wani faifan bidiyo da aka saki a shafukan sada zumunta kuma Daily Trust ta nakalto, Turji ya alakanta karuwar ta’addanci a Zamfara da sauran jihohin Arewa maso Yamma kan manufofin da Matawalle ya tsara a lokacin da yake gwamna.

 

“Duk mutumin da ke zaune a Shinkafi, Zurmi, da Isa (Jihar Sokoto) ba zai iya musanta wannan ikirari ba. Akwai wasu gungun ‘yan bindiga da suka zama ‘yan lelen tsohon gwamnan. Na kore su daga Shinkafi, na kashe shugabansu, Dudu, domin samun dawwamammen zaman lafiya a Shinkafi. Kungiyar na da makamai 200, amma daga baya gwamnan ya karbe su (Yaran Dudu) a gidan gwamnati.

 

“Kuma gwamnati ta gaza nemansu (Yaran Dudu) da su mika makamansu. Sannan akwai Wata kungiya da Bashari Maniya ke jagoranta tana da bindigogi sama da 300.”

 

Turji ya yi ikirarin cewa, ya kwace bindigu 30 daga hannun sansanin ‘yan bindigar da ke karkashin jagorancin Bashari Maniya, kuma kungiyar ba ta taba mika makamanta ga gwamnati ba.

 

A cikin faifan bidiyon, Turji ya kuma yi zargin cewa, wasu shugabannin kungiyoyin ‘yan bindiga da ke cikin yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin Matawalle ta kaddamar sun koma Sokoto da zama bayan sun bai wa yaransu makamai domin ci gaba da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

 

“Ali yaro ne ga Kabiru Maniya, kuma shi ne ke da alhakin kai hare-hare a yankin Tangaza. Bashiri da Kabiru duk suna zaune ne a cikin babban birnin Sokoto, suna jin dadin rayuwarsu. Akwai Wani Buhari, shi ma yana cikin garin Sokoto yana jin dadin rayuwarsa.

 

“Makonni uku da suka wuce, an kama wani kanin Buhari da bindigogi a cikin babban birnin Sokoto. Babu mai musanta wannan. Zan iya fitowa da hujjojin bidiyo wanda ke nuna yadda Kabiru Maniya ke harba manyan bindigogi.

 

“Abin tambaya a yanzu shi ne, ina bindigoginsu bayan da suka ce sun rungumi zaman lafiya sun zauna a garin Sokoto?

 

Ya dace gwamnati ta bayyana wa ’yan Nijeriya wanda ke da alhakin kashe jama’a. Su daina zargin Bello Turji da kashe-kashe da garkuwa da mutane.

 

“Mutanen da ake garkuwa da su a cikin babban birnin Sokoto aka kai su bayan Achida da Goronyo, wa ke da alhakin yin garkuwa da su? Har yanzu Bello Turji ne ? Wanda yake zaune lafiya a Shinkafi?

 

Kokarin jin ta bakin Matawalle domin jin ta bakinsa ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

 

Kiraye-kiraye da yawa da aka yi wa Henshaw Ogubike, mai magana da yawun ma’aikatar tsaro, ya ci tura.

 

Ogbuike, ya aika da sakon tes, inda ya nemi wakilin Daily trust ya yi masa bayanin kiran ta hanyar rubutu (tes) amma bai mayar da martani ga sakon da aka aika masa ba har zuwa lokacin rubuta wannan rahoton.

 

A baya dai Matawalle ya musanta alaka da ‘yan bindigar, ya kuma kara da cewa, gwamnatinsa ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta magance matsalolin tsaro a Zamfara a lokacin da yake kan mulki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan bindigar ZamfaraTabarbarewar tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarkin Katsina Ya Jinjinawa Tinubu Kan Aikin Titin Maraba Zuwa Katsina

Next Post

An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

Related

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

12 hours ago
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

14 hours ago
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
Manyan Labarai

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

17 hours ago
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
Manyan Labarai

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

20 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

1 day ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

2 days ago
Next Post
An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.