ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Matawalle Ce Ta Rura Wutar Ta’addanci A Arewa – Turji

by Sulaiman
2 years ago
Matawalle

Wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, da ke ta’addanci a arewacin Nijeriya, ya zargi karamin ministan tsaro kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da rashin kula da lamarin sulhu da ‘yan bindiga yadda ya kamata a lokacin da yake gwamnan jihar.

 

A lokacin da yake gwamna, Matawalle ya kaddamar da shirin yin afuwa ga ‘yan bindiga inda ya bayyana tattaunawa a matsayin mafi kyawun zabi na magance ta’addancin ‘yan bindiga.

ADVERTISEMENT
  • Jihar Kano Na Shirin Gudanar Da Zaben Ƙananan Hukumomi – Gwamna Abba
  • Shugaba Tinubu Ya Mika Sakon Ta’aziyya ga Kasar Vietnam Kan Rasuwar Nguyễn Phú Trọng

Sai dai kuma daga baya ya janye afuwar, yana mai cewa ‘yan bindigar sun gaza rungumar shirin zaman lafiyar da gwamnatinsa ta yi musu.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A cikin wani faifan bidiyo da aka saki a shafukan sada zumunta kuma Daily Trust ta nakalto, Turji ya alakanta karuwar ta’addanci a Zamfara da sauran jihohin Arewa maso Yamma kan manufofin da Matawalle ya tsara a lokacin da yake gwamna.

 

“Duk mutumin da ke zaune a Shinkafi, Zurmi, da Isa (Jihar Sokoto) ba zai iya musanta wannan ikirari ba. Akwai wasu gungun ‘yan bindiga da suka zama ‘yan lelen tsohon gwamnan. Na kore su daga Shinkafi, na kashe shugabansu, Dudu, domin samun dawwamammen zaman lafiya a Shinkafi. Kungiyar na da makamai 200, amma daga baya gwamnan ya karbe su (Yaran Dudu) a gidan gwamnati.

 

“Kuma gwamnati ta gaza nemansu (Yaran Dudu) da su mika makamansu. Sannan akwai Wata kungiya da Bashari Maniya ke jagoranta tana da bindigogi sama da 300.”

 

Turji ya yi ikirarin cewa, ya kwace bindigu 30 daga hannun sansanin ‘yan bindigar da ke karkashin jagorancin Bashari Maniya, kuma kungiyar ba ta taba mika makamanta ga gwamnati ba.

 

A cikin faifan bidiyon, Turji ya kuma yi zargin cewa, wasu shugabannin kungiyoyin ‘yan bindiga da ke cikin yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin Matawalle ta kaddamar sun koma Sokoto da zama bayan sun bai wa yaransu makamai domin ci gaba da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

 

“Ali yaro ne ga Kabiru Maniya, kuma shi ne ke da alhakin kai hare-hare a yankin Tangaza. Bashiri da Kabiru duk suna zaune ne a cikin babban birnin Sokoto, suna jin dadin rayuwarsu. Akwai Wani Buhari, shi ma yana cikin garin Sokoto yana jin dadin rayuwarsa.

 

“Makonni uku da suka wuce, an kama wani kanin Buhari da bindigogi a cikin babban birnin Sokoto. Babu mai musanta wannan. Zan iya fitowa da hujjojin bidiyo wanda ke nuna yadda Kabiru Maniya ke harba manyan bindigogi.

 

“Abin tambaya a yanzu shi ne, ina bindigoginsu bayan da suka ce sun rungumi zaman lafiya sun zauna a garin Sokoto?

 

Ya dace gwamnati ta bayyana wa ’yan Nijeriya wanda ke da alhakin kashe jama’a. Su daina zargin Bello Turji da kashe-kashe da garkuwa da mutane.

 

“Mutanen da ake garkuwa da su a cikin babban birnin Sokoto aka kai su bayan Achida da Goronyo, wa ke da alhakin yin garkuwa da su? Har yanzu Bello Turji ne ? Wanda yake zaune lafiya a Shinkafi?

 

Kokarin jin ta bakin Matawalle domin jin ta bakinsa ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

 

Kiraye-kiraye da yawa da aka yi wa Henshaw Ogubike, mai magana da yawun ma’aikatar tsaro, ya ci tura.

 

Ogbuike, ya aika da sakon tes, inda ya nemi wakilin Daily trust ya yi masa bayanin kiran ta hanyar rubutu (tes) amma bai mayar da martani ga sakon da aka aika masa ba har zuwa lokacin rubuta wannan rahoton.

 

A baya dai Matawalle ya musanta alaka da ‘yan bindigar, ya kuma kara da cewa, gwamnatinsa ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta magance matsalolin tsaro a Zamfara a lokacin da yake kan mulki.

Matawalle
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.