• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Na Ƙoƙari Wajen Daƙile Hauhawar Farashin Magunguna

by Muhammad
1 year ago
in Kiwon Lafiya, Labarai, Labaran Kasuwanci
0
Ƙudurin Tinubu Na Samar Da Abinci Ba Faɗe A Fatar Baki Ba Ne Kaɗai, Gaskiya Ne – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta yi alkawarin magance tsadar magunguna domin samun sauki ga ‘yan Nijeriya.

Darakta-Janar ta Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC), Farfesa Mojidola Adeyeye, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Lahadi a Abuja.

  • An Shawarci NAFDAC Ta Bullo Da Dabarun Fasaha Wajen Yaki Da Jabun Magunguna
  • Hukumar NAFDAC Ta Bankado Magunguna Marasa Rajista Na Naira Miliyan 15 A Abuja

Sanarwar ta bayyana cewa Adeyey ta ba da wannan tabbacin ne a wata lacca ta yanar gizo da jaridar The Cable ta shirya, domin murnar cika shekaru 10 da kafuwa, mai taken: “Maganin farashin magunguna”.

A cewar Adeyeye, tsadar magunguna da ake yi a kasar nan zai zama tarihi domin hukumar na hada guiwa da masana’antun harhada magunguna domin rage farashin magunguna.

Ta bayyana farfado da masana’antar harhada magunguna ta cikin gida a matsayin maganin tsadar magunguna a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Daraktar ​​ta ce, magungunan da ake samarwa a cikin gida za su fi samun sauki da araha idan aka kwatanta da magungunan da ake shigowa daga waje idan aka farfado da masana’antar harhada magunguna ta cikin gida.

A cewarta, raguwar darajar Naira ya fi tsadar kayan da ake samarwa a cikin gida saboda hauhawar farashin kayayyaki ya sa sayo kayan da ake shigowa da su don samar da su suka yi tsada sosai.

Ta ce, saboda wahalar da ke tattare da sayan dala, farashin magungunan da ake shigowa da su daga kasashen waje ya kai kololuwa.

Adeyeye ta kuma bayyana cewa hukumar ta NAFDAC karkashin jagorancinta ta fara shirin “5 plus 5” wanda ya shafi kamfanonin shigo da magungunan da masana’antun harhada magunguna na cikin gida za su iya samar da su don samun sabuntawa na tsawon shekaru biyar.

Ta ce a cikin shekaru biyar na sabuntawar, dole ne mai shigo da kaya ya yi ƙaura zuwa masana’antu na cikin gida ko kuma ya yi haɗin guiwa da masana’antun cikin gida.

Ta ce sama da kashi 30 cikin 100 na sabbin kamfanoni a Nijeriya sun samo asali ne sakamakon shirin “5 plus 5”, inda ta kara da cewa hakan ya bai wa masu damar shigo da kaya kwarin guiwar gina kamfanoninsu.

Adeyeye ta jaddada cewa wasu tsare-tsare na hukumar NAFDAC na rage tsadar magunguna, inda ta kara da cewa masana’antun cikin gida ba za su iya farawa ba tare da karfafa tsarin doka ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kiwon LafiyaNAFDACNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shettima Zai Je Amurka Don Halartar Taron Kasuwanci Tsakanin Amurka Da Afirka Na 2024

Next Post

Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar

Related

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

1 minute ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

2 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

3 hours ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

12 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

13 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

14 hours ago
Next Post
AFCON 2023: Ekong Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasa Duk Da Rashin Nasarar Nijeriya A Wasan Karshe

Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.