ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shawarci NAFDAC Ta Bullo Da Dabarun Fasaha Wajen Yaki Da Jabun Magunguna

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NAFDAC

‘Yan Nijeriya sun shiga firgici biyo bayan bankado yadda gurbatattun barasa da kayan shaye-shaye ke yaduwa a sassan kasar nan da hukumar kula da ingancin abinci da kwayoyi (NAFDAC) ta yi.

‘Yan Nijeriyan sun nuna damuwarsu a yayin da suke ganawa da wakilanmu inda suka nuna cewa irin wadannan gurbatattun kayayyakin za su yi illa ga sassan jikinsu ba tare da saninsu ba.

  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji
  • An Gano Dukiyar Iyalan Masarautar Saudiyya Ta Fi Ta Masu Arzikin Duniya Biyu Yawa

A kwanakin baya ne NAFDAC ta gano wasu kayayyakin da ake yadawa da suke dauke da gurbatattun abubuwa a ciki da suka kunshi har da nau’ikan barasa kala daban-daban da sauran kayayyakin jabo da basu da amincewa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, an kuma gano cewa akwai wasu nau’ikan kayan da wa’adin amfani da su ya wuce da in aka kuma yi amfani da su za su iya illa ga jikin dan adam da suka kunshi irin nau’ikan madara, yoghurt, da wasu nau’ikan kayan shaye-shaye da sauransu.

A bisa wannan, NAFDAC ta ce, ta rufe wasu shaguna da kamfanoni bisa samunsu da fitar da jabon kaya ga al’umma wanda hakan na barazana ga kiwon lafiyar al’umma.
A bisa wannan, ‘yan Nijeriya da dama sun nuna damuwarsu da kaduwarsu kan bazuwar kayan jabo a cikin kasuwannin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Wata ‘yar kasuwa a jihar Legas, Mr Agatha Onome, ta ce, ta sayi madara a kasuwa amma daga baya ta gano cewa na jabo ne, “Na duba madaran da na saya bayan na dawo gida, a nan ne na fahimci cewa wa’adin amfani da shi ya jima da wucewa.”

Wani dan Nijeriya, Muhammad Adamu ya ce, “Ai ba sabon lamari ba ne yaduwar kayan jabo da gurbattatun kayayyaki a fadin kasar nan. Wasu lokutan ‘yan kasuwa ne ke yada kayan da wa’adin amfani da su ya kara domin guje wa yin asara. A maimakon su dauki yin asarar gara su maida hankali wajen janyo asarar lafiyar jama’a.

“Babban matsalar shi ne sakacin hukumomi, akwai bukatar fito da sabbin dabarun da za su kai ga magance irin wadannan matsalolin yaduwar kayan jabo a kasar nan.”

‘Yan Nijeriyan dai sun shawarci NAFDAC da ta bullo da wasu sabbin manhajojin zamani da za su tursasa amfani da su a iOS da wayoyin Android domin bada dama cikin sauki na gano kayan jabo da sahihai domin rage wa ‘yan Nijeriya firgicin da suke yawan fuskanta.

ShwagDr na cewa, “Ina ganin bullo da manhajar zai bada damar tilasta iOS da wayoyin Android domin bai wa jama’a damar bincika da sake bincika kayan da ke dauke da lambar NAFDAC a jiki.”

Kazalika, darakta-janar na NAFDAC, Farfesa Moji Adeyeye, ta ce, bazuwar kayan jabo a kasuwannin kasar nan na faruwa ne sakamakon rashin ilimi, talauci da kuma matsatsin rayuwa da jama’a ke fuskanta.

Adeyeye, ta ce, hukumar ta samar da manjaha na bincikar sahihancin kaya, ta ce, “Idan kana da wayoyin zamani, za ka iya binciko code din kaya domin gano sahihancinsa ko ingancinsa.”

NAFDAC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Shugaban Maldives: Maldives Ta Samu Goyo Baya Daga Kasar Sin

Shugaban Maldives: Maldives Ta Samu Goyo Baya Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.