ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shawarci NAFDAC Ta Bullo Da Dabarun Fasaha Wajen Yaki Da Jabun Magunguna

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NAFDAC

‘Yan Nijeriya sun shiga firgici biyo bayan bankado yadda gurbatattun barasa da kayan shaye-shaye ke yaduwa a sassan kasar nan da hukumar kula da ingancin abinci da kwayoyi (NAFDAC) ta yi.

‘Yan Nijeriyan sun nuna damuwarsu a yayin da suke ganawa da wakilanmu inda suka nuna cewa irin wadannan gurbatattun kayayyakin za su yi illa ga sassan jikinsu ba tare da saninsu ba.

  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji
  • An Gano Dukiyar Iyalan Masarautar Saudiyya Ta Fi Ta Masu Arzikin Duniya Biyu Yawa

A kwanakin baya ne NAFDAC ta gano wasu kayayyakin da ake yadawa da suke dauke da gurbatattun abubuwa a ciki da suka kunshi har da nau’ikan barasa kala daban-daban da sauran kayayyakin jabo da basu da amincewa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, an kuma gano cewa akwai wasu nau’ikan kayan da wa’adin amfani da su ya wuce da in aka kuma yi amfani da su za su iya illa ga jikin dan adam da suka kunshi irin nau’ikan madara, yoghurt, da wasu nau’ikan kayan shaye-shaye da sauransu.

A bisa wannan, NAFDAC ta ce, ta rufe wasu shaguna da kamfanoni bisa samunsu da fitar da jabon kaya ga al’umma wanda hakan na barazana ga kiwon lafiyar al’umma.
A bisa wannan, ‘yan Nijeriya da dama sun nuna damuwarsu da kaduwarsu kan bazuwar kayan jabo a cikin kasuwannin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Wata ‘yar kasuwa a jihar Legas, Mr Agatha Onome, ta ce, ta sayi madara a kasuwa amma daga baya ta gano cewa na jabo ne, “Na duba madaran da na saya bayan na dawo gida, a nan ne na fahimci cewa wa’adin amfani da shi ya jima da wucewa.”

Wani dan Nijeriya, Muhammad Adamu ya ce, “Ai ba sabon lamari ba ne yaduwar kayan jabo da gurbattatun kayayyaki a fadin kasar nan. Wasu lokutan ‘yan kasuwa ne ke yada kayan da wa’adin amfani da su ya kara domin guje wa yin asara. A maimakon su dauki yin asarar gara su maida hankali wajen janyo asarar lafiyar jama’a.

“Babban matsalar shi ne sakacin hukumomi, akwai bukatar fito da sabbin dabarun da za su kai ga magance irin wadannan matsalolin yaduwar kayan jabo a kasar nan.”

‘Yan Nijeriyan dai sun shawarci NAFDAC da ta bullo da wasu sabbin manhajojin zamani da za su tursasa amfani da su a iOS da wayoyin Android domin bada dama cikin sauki na gano kayan jabo da sahihai domin rage wa ‘yan Nijeriya firgicin da suke yawan fuskanta.

ShwagDr na cewa, “Ina ganin bullo da manhajar zai bada damar tilasta iOS da wayoyin Android domin bai wa jama’a damar bincika da sake bincika kayan da ke dauke da lambar NAFDAC a jiki.”

Kazalika, darakta-janar na NAFDAC, Farfesa Moji Adeyeye, ta ce, bazuwar kayan jabo a kasuwannin kasar nan na faruwa ne sakamakon rashin ilimi, talauci da kuma matsatsin rayuwa da jama’a ke fuskanta.

Adeyeye, ta ce, hukumar ta samar da manjaha na bincikar sahihancin kaya, ta ce, “Idan kana da wayoyin zamani, za ka iya binciko code din kaya domin gano sahihancinsa ko ingancinsa.”

NAFDAC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Shugaban Maldives: Maldives Ta Samu Goyo Baya Daga Kasar Sin

Shugaban Maldives: Maldives Ta Samu Goyo Baya Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.