• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Na Ƙoƙari Wajen Daƙile Hauhawar Farashin Magunguna

by Muhammad
1 year ago
in Kiwon Lafiya, Labarai, Labaran Kasuwanci
0
Ƙudurin Tinubu Na Samar Da Abinci Ba Faɗe A Fatar Baki Ba Ne Kaɗai, Gaskiya Ne – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta yi alkawarin magance tsadar magunguna domin samun sauki ga ‘yan Nijeriya.

Darakta-Janar ta Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC), Farfesa Mojidola Adeyeye, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Lahadi a Abuja.

  • An Shawarci NAFDAC Ta Bullo Da Dabarun Fasaha Wajen Yaki Da Jabun Magunguna
  • Hukumar NAFDAC Ta Bankado Magunguna Marasa Rajista Na Naira Miliyan 15 A Abuja

Sanarwar ta bayyana cewa Adeyey ta ba da wannan tabbacin ne a wata lacca ta yanar gizo da jaridar The Cable ta shirya, domin murnar cika shekaru 10 da kafuwa, mai taken: “Maganin farashin magunguna”.

A cewar Adeyeye, tsadar magunguna da ake yi a kasar nan zai zama tarihi domin hukumar na hada guiwa da masana’antun harhada magunguna domin rage farashin magunguna.

Ta bayyana farfado da masana’antar harhada magunguna ta cikin gida a matsayin maganin tsadar magunguna a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

Daraktar ​​ta ce, magungunan da ake samarwa a cikin gida za su fi samun sauki da araha idan aka kwatanta da magungunan da ake shigowa daga waje idan aka farfado da masana’antar harhada magunguna ta cikin gida.

A cewarta, raguwar darajar Naira ya fi tsadar kayan da ake samarwa a cikin gida saboda hauhawar farashin kayayyaki ya sa sayo kayan da ake shigowa da su don samar da su suka yi tsada sosai.

Ta ce, saboda wahalar da ke tattare da sayan dala, farashin magungunan da ake shigowa da su daga kasashen waje ya kai kololuwa.

Adeyeye ta kuma bayyana cewa hukumar ta NAFDAC karkashin jagorancinta ta fara shirin “5 plus 5” wanda ya shafi kamfanonin shigo da magungunan da masana’antun harhada magunguna na cikin gida za su iya samar da su don samun sabuntawa na tsawon shekaru biyar.

Ta ce a cikin shekaru biyar na sabuntawar, dole ne mai shigo da kaya ya yi ƙaura zuwa masana’antu na cikin gida ko kuma ya yi haɗin guiwa da masana’antun cikin gida.

Ta ce sama da kashi 30 cikin 100 na sabbin kamfanoni a Nijeriya sun samo asali ne sakamakon shirin “5 plus 5”, inda ta kara da cewa hakan ya bai wa masu damar shigo da kaya kwarin guiwar gina kamfanoninsu.

Adeyeye ta jaddada cewa wasu tsare-tsare na hukumar NAFDAC na rage tsadar magunguna, inda ta kara da cewa masana’antun cikin gida ba za su iya farawa ba tare da karfafa tsarin doka ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kiwon LafiyaNAFDACNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shettima Zai Je Amurka Don Halartar Taron Kasuwanci Tsakanin Amurka Da Afirka Na 2024

Next Post

Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar

Related

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

33 minutes ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

4 hours ago
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

6 hours ago
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Labarai

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

7 hours ago
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi
Labarai

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

8 hours ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Manyan Labarai

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

9 hours ago
Next Post
AFCON 2023: Ekong Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasa Duk Da Rashin Nasarar Nijeriya A Wasan Karshe

Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.