• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Na Ƙoƙari Wajen Daƙile Hauhawar Farashin Magunguna

by Muhammad
1 year ago
in Kiwon Lafiya, Labarai, Labaran Kasuwanci
0
Ƙudurin Tinubu Na Samar Da Abinci Ba Faɗe A Fatar Baki Ba Ne Kaɗai, Gaskiya Ne – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta yi alkawarin magance tsadar magunguna domin samun sauki ga ‘yan Nijeriya.

Darakta-Janar ta Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC), Farfesa Mojidola Adeyeye, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Lahadi a Abuja.

  • An Shawarci NAFDAC Ta Bullo Da Dabarun Fasaha Wajen Yaki Da Jabun Magunguna
  • Hukumar NAFDAC Ta Bankado Magunguna Marasa Rajista Na Naira Miliyan 15 A Abuja

Sanarwar ta bayyana cewa Adeyey ta ba da wannan tabbacin ne a wata lacca ta yanar gizo da jaridar The Cable ta shirya, domin murnar cika shekaru 10 da kafuwa, mai taken: “Maganin farashin magunguna”.

A cewar Adeyeye, tsadar magunguna da ake yi a kasar nan zai zama tarihi domin hukumar na hada guiwa da masana’antun harhada magunguna domin rage farashin magunguna.

Ta bayyana farfado da masana’antar harhada magunguna ta cikin gida a matsayin maganin tsadar magunguna a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Daraktar ​​ta ce, magungunan da ake samarwa a cikin gida za su fi samun sauki da araha idan aka kwatanta da magungunan da ake shigowa daga waje idan aka farfado da masana’antar harhada magunguna ta cikin gida.

A cewarta, raguwar darajar Naira ya fi tsadar kayan da ake samarwa a cikin gida saboda hauhawar farashin kayayyaki ya sa sayo kayan da ake shigowa da su don samar da su suka yi tsada sosai.

Ta ce, saboda wahalar da ke tattare da sayan dala, farashin magungunan da ake shigowa da su daga kasashen waje ya kai kololuwa.

Adeyeye ta kuma bayyana cewa hukumar ta NAFDAC karkashin jagorancinta ta fara shirin “5 plus 5” wanda ya shafi kamfanonin shigo da magungunan da masana’antun harhada magunguna na cikin gida za su iya samar da su don samun sabuntawa na tsawon shekaru biyar.

Ta ce a cikin shekaru biyar na sabuntawar, dole ne mai shigo da kaya ya yi ƙaura zuwa masana’antu na cikin gida ko kuma ya yi haɗin guiwa da masana’antun cikin gida.

Ta ce sama da kashi 30 cikin 100 na sabbin kamfanoni a Nijeriya sun samo asali ne sakamakon shirin “5 plus 5”, inda ta kara da cewa hakan ya bai wa masu damar shigo da kaya kwarin guiwar gina kamfanoninsu.

Adeyeye ta jaddada cewa wasu tsare-tsare na hukumar NAFDAC na rage tsadar magunguna, inda ta kara da cewa masana’antun cikin gida ba za su iya farawa ba tare da karfafa tsarin doka ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kiwon LafiyaNAFDACNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shettima Zai Je Amurka Don Halartar Taron Kasuwanci Tsakanin Amurka Da Afirka Na 2024

Next Post

Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

7 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
AFCON 2023: Ekong Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasa Duk Da Rashin Nasarar Nijeriya A Wasan Karshe

Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.