ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Soki Tarayyar Turai Kan Zaben 2023

by Muhammad
2 years ago
Gwamnatin Nijeriya

Fadar shugaban Nijeriya ta yi fatali da wani rahoto da kungiyar Tarayyar Turai, EU, ta fitar da ya ce akwai kura-kurai kan zaben kasar na 2023.

An gudanar da zaben shugaban kasar ne a watan Fabrairu inda hukumar zabe mai zaman kanta ta Nijeriya, INEC, ta ayyana dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara.

  • Tinubu Ya Koma Abuja Bayan Ziyarar Faransa, Landan Da Legas
  • Kada Ka Nada Tsohon Gwamna Mukamin Minista -Kungiya Ga Tinubu

TRT Afrika ta rawaito cewa, a rahoton da jagoran kungiyar Tarayyar Turai Barry Andrews ya fitar ya ce an tafka kura-kurai a zaben don haka ba shi da sahihancin da ya kamata.

ADVERTISEMENT

Amma a wata sanarwa da kakakin shugaban kasar Mr Dele Alake ya fitar ranar Lahadi, ya yi watsi da rahoton Tarayyar Turan yana mai cewa ya nuna son kai karara.

Mr Alake ya ce da ma tun a watan Mayu suka sanar da ‘yan Nijeriya cewa wata kungiya na shirin fitar da rahoto da zummar bayyana zaben kasar a matsayin gurbatacce.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

“Yanzu tun da wannan kungiya ta fitar da abin da ta yi ikirarin cewa shi ne rahotonta na karshe, muna iya sanar da ‘yan Nijeriya da duniya cewa muna sane da tuggun Tarayyar Turai na jaddada son kai da ikirarinta mara tushe kan sakamakon zaben,” in ji kakakin shugaban kasar.

Ya kara da cewa abin takaici ne yadda Tarayyar Turai, wadda ta tura masu sanya ido da ba su kai 50 ba a kasa mai akwatunan zabe fiye da 176,000, ta fito tana cewa zaben kasar bai inganta ba.

“Muna so mu sani sannan mu tambayi EU, ta yaya ta hada rahotonta na karshe bayan kuwa masu sanya idanunta a zaben kalilan ne wadanda, babu shakka, sun dogara ne da jita-jita da wane-ya-ji-ga-wane da masu sharhi a soshiyal midiya da ba su da masaniya da kuma masu magana da yawun ‘yan hamayya,” a cewar sanarwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Ku Dakata Da Gine-Gine A Filayen Gwamnati Da Makarantu – Abba Gida-Gida

Asibitin Yara Na Hasiya Bayero Zai Dawo Aiki – Abba Gida-Gida

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.