• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Sun Kawar Da Fargabar Ɓallewar Madatsun Ruwa A Arewa

by Sulaiman
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Sun Kawar Da Fargabar Ɓallewar Madatsun Ruwa A Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manyan jami’an gwamnatin tarayya da na jihohi sun baiwa al’ummomin da ke zaune a yankin manyan madatsun ruwa a arewacin Nijeriya tabbacin kubuta daga fargabar da ke tattare da su na ballewar madatsun.

 

Tun bayan afkuwar bala’in ballewar madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno, al’umma sun shiga fargaba, inda suka yi zargin cewa, madatsun ruwa da ke sauran yankunan Arewa na cikin wani mummunan hali.

  • Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon
  • Akwai Bukatar Shugabannin Arewa Su Farka – Sarkin Fawa

Ballewar madatsar ruwa da ta taba afkuwa a garin Goronyo da kewayen jihar Sokoto, ta sanya mazauna garin cikin damuwa bayan bala’in Borno, ganin cewa, hakan na iya afkuwa da su.

 

Labarai Masu Nasaba

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

Saboda ire-iren wannan firgici, Ministan Albarkatun Ruwa, Engr Joseph Utsev ya kai ziyarar gani da ido wasu manya daga cikin madatsun ruwa da ke Arewacin Nijeriya, inda ya tabbatar da cewa, babu wata fargaba.

 

“Ana ta yada irin wannan jita-jita game da madatsar ruwa ta Dandin Kowa da ke Gombe amma da muka isa wurin sai aka gano cewa, jita-jita ce kuma karya ce.”

 

Dam din Dadin Kowa da ke jihar Gombe a kwanakin baya ya haifar da fargaba bayan da rahotanni suka bayyana cewa, zai iya ballewa sakamakon mamakon ruwan sama da ke zuba.

 

Daga cikin madatsun ruwan da aka bincika don gujewa irin bala’in da ya afku a Borno sun hada da:

 

Madatsun ruwa dake karamar hukumar Gusau, Bakalori dake karamar hukumar Maradun da Dangulbi dake karamar hukumar Maru a jihar Zamfara.

 

A jihar Kano akwai Babbar Madatsar ruwa ta Tiga, Bagwai da Challawa.

 

Madatsar ruwa ta Asa da ke Ilorin a jihar Kwara, an tabbatar cewa, tana cikin kyakkyawar kula.

 

A jihar Neja, akwai manyan Madatsun ruwa guda hudu da suka hada da Kainji, Jebba, Shiroro da Zungeru.

 

Sai dai Ministan Albarkatun Ruwa, Engr Joseph Utsev ya tabbatar wa jama’a cewa, babu wani abin fargaba a duk madatsun ruwan.

 

A ziyarar da ministan ya kai a baya bayan nan, ya tabbatar da cewa, gwamnatin tarayya na daukar matakan kare madatsar ruwan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaAmbaliyar RuwaFargabar ballewar madatsar ruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon

Next Post

Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Borno

Related

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
Manyan Labarai

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

4 hours ago
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Manyan Labarai

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

21 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

1 day ago
Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

2 days ago
Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
Manyan Labarai

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

2 days ago
nijeriya
Manyan Labarai

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

2 days ago
Next Post
Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Borno

Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin 'Yan Ta'adda A Borno

LABARAI MASU NASABA

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

June 15, 2025
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

June 15, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

June 15, 2025
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

June 15, 2025
UEFA

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

June 15, 2025
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

June 15, 2025
Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

June 14, 2025
Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

June 14, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

June 14, 2025
Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.