• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Sun Kawar Da Fargabar Ɓallewar Madatsun Ruwa A Arewa

bySulaiman
1 year ago
inManyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Sun Kawar Da Fargabar Ɓallewar Madatsun Ruwa A Arewa

Manyan jami’an gwamnatin tarayya da na jihohi sun baiwa al’ummomin da ke zaune a yankin manyan madatsun ruwa a arewacin Nijeriya tabbacin kubuta daga fargabar da ke tattare da su na ballewar madatsun.

 

Tun bayan afkuwar bala’in ballewar madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno, al’umma sun shiga fargaba, inda suka yi zargin cewa, madatsun ruwa da ke sauran yankunan Arewa na cikin wani mummunan hali.

  • Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon
  • Akwai Bukatar Shugabannin Arewa Su Farka – Sarkin Fawa

Ballewar madatsar ruwa da ta taba afkuwa a garin Goronyo da kewayen jihar Sokoto, ta sanya mazauna garin cikin damuwa bayan bala’in Borno, ganin cewa, hakan na iya afkuwa da su.

 

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

Saboda ire-iren wannan firgici, Ministan Albarkatun Ruwa, Engr Joseph Utsev ya kai ziyarar gani da ido wasu manya daga cikin madatsun ruwa da ke Arewacin Nijeriya, inda ya tabbatar da cewa, babu wata fargaba.

 

“Ana ta yada irin wannan jita-jita game da madatsar ruwa ta Dandin Kowa da ke Gombe amma da muka isa wurin sai aka gano cewa, jita-jita ce kuma karya ce.”

 

Dam din Dadin Kowa da ke jihar Gombe a kwanakin baya ya haifar da fargaba bayan da rahotanni suka bayyana cewa, zai iya ballewa sakamakon mamakon ruwan sama da ke zuba.

 

Daga cikin madatsun ruwan da aka bincika don gujewa irin bala’in da ya afku a Borno sun hada da:

 

Madatsun ruwa dake karamar hukumar Gusau, Bakalori dake karamar hukumar Maradun da Dangulbi dake karamar hukumar Maru a jihar Zamfara.

 

A jihar Kano akwai Babbar Madatsar ruwa ta Tiga, Bagwai da Challawa.

 

Madatsar ruwa ta Asa da ke Ilorin a jihar Kwara, an tabbatar cewa, tana cikin kyakkyawar kula.

 

A jihar Neja, akwai manyan Madatsun ruwa guda hudu da suka hada da Kainji, Jebba, Shiroro da Zungeru.

 

Sai dai Ministan Albarkatun Ruwa, Engr Joseph Utsev ya tabbatar wa jama’a cewa, babu wani abin fargaba a duk madatsun ruwan.

 

A ziyarar da ministan ya kai a baya bayan nan, ya tabbatar da cewa, gwamnatin tarayya na daukar matakan kare madatsar ruwan.

Tags: AlmundahanaAmbaliyar RuwaFargabar ballewar madatsar ruwa
ShareTweetSendShare
Sulaiman

Sulaiman

Related

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

5 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

6 hours ago
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 
Manyan Labarai

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

18 hours ago
Next Post
Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Borno

Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin 'Yan Ta'adda A Borno

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.