• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Sun Kawar Da Fargabar Ɓallewar Madatsun Ruwa A Arewa

by Sulaiman
1 year ago
Madatsun ruwa

Manyan jami’an gwamnatin tarayya da na jihohi sun baiwa al’ummomin da ke zaune a yankin manyan madatsun ruwa a arewacin Nijeriya tabbacin kubuta daga fargabar da ke tattare da su na ballewar madatsun.

 

Tun bayan afkuwar bala’in ballewar madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno, al’umma sun shiga fargaba, inda suka yi zargin cewa, madatsun ruwa da ke sauran yankunan Arewa na cikin wani mummunan hali.

  • Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon
  • Akwai Bukatar Shugabannin Arewa Su Farka – Sarkin Fawa

Ballewar madatsar ruwa da ta taba afkuwa a garin Goronyo da kewayen jihar Sokoto, ta sanya mazauna garin cikin damuwa bayan bala’in Borno, ganin cewa, hakan na iya afkuwa da su.

 

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Saboda ire-iren wannan firgici, Ministan Albarkatun Ruwa, Engr Joseph Utsev ya kai ziyarar gani da ido wasu manya daga cikin madatsun ruwa da ke Arewacin Nijeriya, inda ya tabbatar da cewa, babu wata fargaba.

 

“Ana ta yada irin wannan jita-jita game da madatsar ruwa ta Dandin Kowa da ke Gombe amma da muka isa wurin sai aka gano cewa, jita-jita ce kuma karya ce.”

 

Dam din Dadin Kowa da ke jihar Gombe a kwanakin baya ya haifar da fargaba bayan da rahotanni suka bayyana cewa, zai iya ballewa sakamakon mamakon ruwan sama da ke zuba.

 

Daga cikin madatsun ruwan da aka bincika don gujewa irin bala’in da ya afku a Borno sun hada da:

 

Madatsun ruwa dake karamar hukumar Gusau, Bakalori dake karamar hukumar Maradun da Dangulbi dake karamar hukumar Maru a jihar Zamfara.

 

A jihar Kano akwai Babbar Madatsar ruwa ta Tiga, Bagwai da Challawa.

 

Madatsar ruwa ta Asa da ke Ilorin a jihar Kwara, an tabbatar cewa, tana cikin kyakkyawar kula.

 

A jihar Neja, akwai manyan Madatsun ruwa guda hudu da suka hada da Kainji, Jebba, Shiroro da Zungeru.

 

Sai dai Ministan Albarkatun Ruwa, Engr Joseph Utsev ya tabbatar wa jama’a cewa, babu wani abin fargaba a duk madatsun ruwan.

 

A ziyarar da ministan ya kai a baya bayan nan, ya tabbatar da cewa, gwamnatin tarayya na daukar matakan kare madatsar ruwan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Next Post
Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Borno

Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin 'Yan Ta'adda A Borno

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.