ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ita Kadai Ba Za Ta Iya Daukar Dawainiyar Kudaden Ilimi Ba – Minista

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
ilimi

Ministan ilimi, Farfesa Tahir Mamman, ya shaida cewar gwamnatin tarayya ita kadai ba za ta iya daukan dawainiyar kudaden da sashin ilimi ke bukata a Nijeriya ba.

Ya shaida hakan ne a Abuja a yayin wani taro da aka shirya domin karrama Dakta Emeka Offor da matarsa, Dakta Adaora Offor wadanda suka samu lambar yabon digiri ta karramawa a bangaren tafiyar da harkokin kasuwanci da kuma shawarorin zamantakewa wanda jami’ar Nigeria Nsukka (UNN) da jami’ar Nnamdi Azikiwe (NAU), Awka suka ba su.

  • Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Fityanul Islam Ta Zaburar Da Musulmi Kan Bin Addini

Ministan ya ce gwamnati na kashe maguden kudade wajen daukan nauyin ilimi, don haka akwai bukatar daidaikun mutane da masu hannu da shuni da su kwaikwayi abun da Mista Offor da matarsa suka yi ta hanyar gidauniyarsu na taimakon ilimi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Ma’aikatarmu tana karfafan irin wannan karamcin, saboda gwamnati ba za ta iya dauke dawainiyar kudaden ilimi ita kadai ba, domin tana ba da gudunma-wa sosai.

“Wannan dalilin ne ya sanya mutane irin su Emeka Offor da matarsa suka shigo cikin lamarin, sannan akwai bukatar a karfafa musu guiwa. Na yi amanar wannan shi ne irin misalin kashe kudade ta hanyoyin da suka dace, don haka, ina kira ga sauran masu hannu da shuni da su yi koyi da abun da su din suka yi.”

LABARAI MASU NASABA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Yayin da jami’ar UNN ta amshi naira miliyan 100 domin harkokin da suka shafi zurfafa bincike da nazarin ilimi tare da masana harkokin kasuwanci domin ingant-awa da tabbatar da yin tasiri a tsangayar koyar da ilimin harkokin gudanar da kasuwanci, inda ita kuma jami’ar NAU ta amshi naira miliyan 50 a matsayin tal-lafin kula da walwalar zawarawa, yara da suke fama da bukata ta musamman da kuma sauran jama’a da ke cikin yanayi na fatara.

Mai ba da tallafin, Cif Offor ya ce, wannan tallafin ba shi ne na karshe ba, kuma za su ci gaba da yin duk mai yiyuwa domin taimaka wa jami’o’in Nijeriya.

Ya ce, “Wannan tallafin na daga cikin manufarmu na ganin mun taimaka wa ilimi a manyan matakai a Nijeriya,” sai ya nemi karin hadin guiwa a tsakanin gidauniyar-sa ta SEOF da kuma jami’o’in UNN da NAU.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
Ilimi

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
Next Post
Foamy Urine

Matsalar Da Ke Haifar Da Fitsari Mai Kumfa (Foamy Urine)

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.