• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya na hasashen samun kudin shiga na naira tiriliyan 34.8 a kudirin kasafin kudin 2025. Kudirin ya kuma tsara dabarun sake fasalin bashi da nufin ‘yantar da kudade don ci gaban ababen more rayuwa.

Wannan tsarin yana daya daga cikin muhimman abubuwan da aka tsara na 2025-2027, matsakaaicin dubarun harkokin kudade, wanda majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da shi a ranar Alhamis.

  • Gwamnati Ta Ɗage Haramcin Tura Masu Yi Wa Ƙasa Hidima Bankuna Da Sauran Masana’antu 
  • Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Za a mika kudirin kasafin kudin 2025 na naira tiriliyan 47.9 ga majalisar dokoki ta kasa domin tantancewa.

A cewar takardar da ofishin kasafin kudi na tarayya ya fitar, ana sa ran biyan basussuka, saboda yawan basussukan da ake bin kasar da kuma yadda babban bankin Nijeriya (CBN) ya kara kudin ruwa zuwa kashi 27.25.

Kudirin dokar ya zayyana yadda za a samu manyan kudaden shiga da manufofin kashewa a cikin 2025.

Labarai Masu Nasaba

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

A karkashin kudaden shiga, gwamnatin tarayya na shirin samun naira tiriliyan 34.8 da naira tiriliyan 19.6 da naira tiriliyan 5.7 daga harajin man fetur da bangarori wadanda ba na man fetur ba, naira tiriliyan 2.87 daga kamfanonin mallakar gwamnati, naira tiriliyan 3.6 daga hanyoyin samun kudaden shiga masu zaman kansu da kuma naira tiriliyan 4.8 daga wasu hanyoyin.

Kudirin kashe kudi na gwamnati na shekara mai zuwa shi ne naira tiriliyan 47.9, wanda ya kunshi naira tiriliyan 14.2 na biyan bashi, naira tiriliyan 16.4 za a kashe wajen gudanar da manyan ayyuka, naira tiriliyan 15.38 na hidimar basussuka da kuma naira tiriliyan 2 na sauran abubuwan da za a yi.

Gwamnati ta amince da kalubalen tattara kudaden shiga, karancin mai da iskar gas, da hauhawar farashin tallafin man fetur a matsayin masu bayar da gudummawa ga gibin kasafin kudin tarayya.

Sai dai ana sa ran sauye-sauyen da aka yi a baya-bayan nan da suka hada da cire tallafin man fetur, da rage harajin da ake samu, da karuwar yawan danyen mai da ake hakowa za su rage matsin tattalin arziki.

Domin cike gibin kasafin kudin, gwamnati za ta ciyo bashi mai sassauci da kuma aiwatar da matakan tattara kudaden shiga.

Gwamnati na shirin kara zage damtse wajen inganta harkokin kudi ta hanyar karfafa tsarin kasafin kudi da kuma duba yadda ma’aikatu da hukumomi gwamnati suke kashe kudade.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiTarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Halartar Shugaba Xi Taron APEC Da G20, Da Ziyarar Aiki A Peru Da Brazil Sun Kasance Wata Hanyar Sada Zumunta Da Hadin Gwiwa

Next Post

Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Related

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

55 minutes ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

10 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

11 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

12 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

13 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

15 hours ago
Next Post
Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.