• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Gidaje Masu Saukin Kudi 1,250 A Jihohi Hudu

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bakin ma’aikatar gidaje da raya birane, ta sanar da fara aikin gina gidaje masu saukin kudi fiye da 1,250 a jihohi hudu na arewacin Nijeriya a tsarin da aka yi wa lakabi da ‘Renewed Hope Cities’.
A ranar Laraba ta wannan makon aka shirya kaddamar da shirin a jihar Katsina daga nan kuma za a zarce Jihar Gonmbe inda nan ma za a kaddamar da aikin gina gidajen a ranar 25 ga watan Mayu 2024.

Ministan gidaje da raya birane, Alhaji Ahmed Dangiwa ya bayyana haka a takardar sanarwar da ya raba wa manema labarai, ya ce tuni aka kammala dukakn yarjejeniyar kwangilar tare da bayar da kudin somin tabi ga dukkan ‘yan kwangilar da suka samu aikin gina gidajen a fadin arewacin Nijeriya.

  • Gwamnatin Kwara Ta Tasa Keyar Mabarata 158 Zuwa Jihohinsu Na Asali
  • Nijeriya Ta Yi Hankali Da Hadari Da Santsin Kwarin Silikon Na Amurka

Shirin ya biyo bayan kaddamarwa da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya yi ne na gina gidaje 3,112 a unguwar Karsana da ke babban birnin tarayya, Abuja a watnb Fabrairu na shekarar 2024.

Sanarwar wanda da jami’in watsa labarai na ministan, Mark Chieshe, ya sanya wa hannu ya kuma jaddada aniyar gwamnatin Tinubu na samar da gidaje masu saukin kudi a fadin kasar nan tare da kuma samar wa matasanmu aikin yi wanda hakan zai bunkasa tattalin arzikin kasa.

Sanarwa ta kuma ce, “Ministan zai kaddamar da fara aikin gina gidajen kamar haka, gidaje 250 a Katsina a ranar Laraba 22 ga watan Mayu, 2024, sai gidaje 500 a garin Kano a ranar Alhamis 23 ga watan Mayu 2024 sai kuma gidaje 250 a Jihar Yobe a ranar Juma’a 24 ga watan Mayu 2024, daga nan kuma sai Jihar Gombe inda za a gina gidaje 250 a ranar 25 ga watan Mayu. Dukkan gidajen an yi musu lakabi da ‘Renewed Hope Estate’.

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

“Mun tsayu na ganin cika alkawarin da Shugaban Kasa Tinubu ya yi wa ‘yan Nijeriya na mayar da fadin kasar nan fagen gine gine, ta nan kuma muna sa ran a samar wa matasa aikin yi.,” in ji MInistan

Ya kuma kara da cewa, zuwa yanzu ma’aikatar ta bayar da kwangilar gina gidaje fiye da 3,500 a jihohi 13 na kasar nan tun daga watan Disamba na shekarar 2023 a karkashin kasafin kudin kasa da aka gabatar na cike gurbi.

Jihohin sun kuma hada da Katsina, Sokoto, Yobe, Gombe, Nasarawa, Benue, Osun, Oyo, Abia, Ebonyi, Delta da Akwa Ibom.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bunkasa Tattalin ArzikiGidajeTsadar yanayi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Kudin Zimbabwe Ya Jinjinawa Gudummawar Masu Zuba Jari Daga Sin

Next Post

Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

4 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

2 weeks ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

3 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

3 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 weeks ago
Next Post
Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.