ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Gidaje Masu Saukin Kudi 1,250 A Jihohi Hudu

by Bello Hamza
1 year ago
nijeriya

Gwamnatin tarayya ta bakin ma’aikatar gidaje da raya birane, ta sanar da fara aikin gina gidaje masu saukin kudi fiye da 1,250 a jihohi hudu na arewacin Nijeriya a tsarin da aka yi wa lakabi da ‘Renewed Hope Cities’.
A ranar Laraba ta wannan makon aka shirya kaddamar da shirin a jihar Katsina daga nan kuma za a zarce Jihar Gonmbe inda nan ma za a kaddamar da aikin gina gidajen a ranar 25 ga watan Mayu 2024.

Ministan gidaje da raya birane, Alhaji Ahmed Dangiwa ya bayyana haka a takardar sanarwar da ya raba wa manema labarai, ya ce tuni aka kammala dukakn yarjejeniyar kwangilar tare da bayar da kudin somin tabi ga dukkan ‘yan kwangilar da suka samu aikin gina gidajen a fadin arewacin Nijeriya.

  • Gwamnatin Kwara Ta Tasa Keyar Mabarata 158 Zuwa Jihohinsu Na Asali
  • Nijeriya Ta Yi Hankali Da Hadari Da Santsin Kwarin Silikon Na Amurka

Shirin ya biyo bayan kaddamarwa da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya yi ne na gina gidaje 3,112 a unguwar Karsana da ke babban birnin tarayya, Abuja a watnb Fabrairu na shekarar 2024.

ADVERTISEMENT

Sanarwar wanda da jami’in watsa labarai na ministan, Mark Chieshe, ya sanya wa hannu ya kuma jaddada aniyar gwamnatin Tinubu na samar da gidaje masu saukin kudi a fadin kasar nan tare da kuma samar wa matasanmu aikin yi wanda hakan zai bunkasa tattalin arzikin kasa.

Sanarwa ta kuma ce, “Ministan zai kaddamar da fara aikin gina gidajen kamar haka, gidaje 250 a Katsina a ranar Laraba 22 ga watan Mayu, 2024, sai gidaje 500 a garin Kano a ranar Alhamis 23 ga watan Mayu 2024 sai kuma gidaje 250 a Jihar Yobe a ranar Juma’a 24 ga watan Mayu 2024, daga nan kuma sai Jihar Gombe inda za a gina gidaje 250 a ranar 25 ga watan Mayu. Dukkan gidajen an yi musu lakabi da ‘Renewed Hope Estate’.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

“Mun tsayu na ganin cika alkawarin da Shugaban Kasa Tinubu ya yi wa ‘yan Nijeriya na mayar da fadin kasar nan fagen gine gine, ta nan kuma muna sa ran a samar wa matasa aikin yi.,” in ji MInistan

Ya kuma kara da cewa, zuwa yanzu ma’aikatar ta bayar da kwangilar gina gidaje fiye da 3,500 a jihohi 13 na kasar nan tun daga watan Disamba na shekarar 2023 a karkashin kasafin kudin kasa da aka gabatar na cike gurbi.

Jihohin sun kuma hada da Katsina, Sokoto, Yobe, Gombe, Nasarawa, Benue, Osun, Oyo, Abia, Ebonyi, Delta da Akwa Ibom.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Tattalin Arziki

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
Tattalin Arziki

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Next Post
Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

LABARAI MASU NASABA

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.