• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Gidaje Masu Saukin Kudi 1,250 A Jihohi Hudu

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bakin ma’aikatar gidaje da raya birane, ta sanar da fara aikin gina gidaje masu saukin kudi fiye da 1,250 a jihohi hudu na arewacin Nijeriya a tsarin da aka yi wa lakabi da ‘Renewed Hope Cities’.
A ranar Laraba ta wannan makon aka shirya kaddamar da shirin a jihar Katsina daga nan kuma za a zarce Jihar Gonmbe inda nan ma za a kaddamar da aikin gina gidajen a ranar 25 ga watan Mayu 2024.

Ministan gidaje da raya birane, Alhaji Ahmed Dangiwa ya bayyana haka a takardar sanarwar da ya raba wa manema labarai, ya ce tuni aka kammala dukakn yarjejeniyar kwangilar tare da bayar da kudin somin tabi ga dukkan ‘yan kwangilar da suka samu aikin gina gidajen a fadin arewacin Nijeriya.

  • Gwamnatin Kwara Ta Tasa Keyar Mabarata 158 Zuwa Jihohinsu Na Asali
  • Nijeriya Ta Yi Hankali Da Hadari Da Santsin Kwarin Silikon Na Amurka

Shirin ya biyo bayan kaddamarwa da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya yi ne na gina gidaje 3,112 a unguwar Karsana da ke babban birnin tarayya, Abuja a watnb Fabrairu na shekarar 2024.

Sanarwar wanda da jami’in watsa labarai na ministan, Mark Chieshe, ya sanya wa hannu ya kuma jaddada aniyar gwamnatin Tinubu na samar da gidaje masu saukin kudi a fadin kasar nan tare da kuma samar wa matasanmu aikin yi wanda hakan zai bunkasa tattalin arzikin kasa.

Sanarwa ta kuma ce, “Ministan zai kaddamar da fara aikin gina gidajen kamar haka, gidaje 250 a Katsina a ranar Laraba 22 ga watan Mayu, 2024, sai gidaje 500 a garin Kano a ranar Alhamis 23 ga watan Mayu 2024 sai kuma gidaje 250 a Jihar Yobe a ranar Juma’a 24 ga watan Mayu 2024, daga nan kuma sai Jihar Gombe inda za a gina gidaje 250 a ranar 25 ga watan Mayu. Dukkan gidajen an yi musu lakabi da ‘Renewed Hope Estate’.

Labarai Masu Nasaba

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

“Mun tsayu na ganin cika alkawarin da Shugaban Kasa Tinubu ya yi wa ‘yan Nijeriya na mayar da fadin kasar nan fagen gine gine, ta nan kuma muna sa ran a samar wa matasa aikin yi.,” in ji MInistan

Ya kuma kara da cewa, zuwa yanzu ma’aikatar ta bayar da kwangilar gina gidaje fiye da 3,500 a jihohi 13 na kasar nan tun daga watan Disamba na shekarar 2023 a karkashin kasafin kudin kasa da aka gabatar na cike gurbi.

Jihohin sun kuma hada da Katsina, Sokoto, Yobe, Gombe, Nasarawa, Benue, Osun, Oyo, Abia, Ebonyi, Delta da Akwa Ibom.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bunkasa Tattalin ArzikiGidajeTsadar yanayi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Kudin Zimbabwe Ya Jinjinawa Gudummawar Masu Zuba Jari Daga Sin

Next Post

Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

Related

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

7 hours ago
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
Tattalin Arziki

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

7 days ago
Dangote
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

2 weeks ago
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote
Tattalin Arziki

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

2 weeks ago
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
Tattalin Arziki

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

3 weeks ago
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
Tattalin Arziki

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

3 weeks ago
Next Post
Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.