• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Jakadan Burkina Faso Kan Kisan ‘Yan Nijeriya 16

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Jakadan Burkina Faso Kan Kisan ‘Yan Nijeriya 16
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijrtiya ta fara daukan kwakkwaran matakai domin bankado batutuwan da suke mamaye da kisan ‘yan Nijeriya 16 da suka yi niyyar zuwa ziyarar musulunci a Kaolack da ke kasar Senegal da ake zargin jami’an tsaron Burkina Faso ne suka kashe su.

 

Karamin ministan kula da harkokin cikin gida, Ambasada Zubairu Dada shi ne ya gayyaci jakadan na Burkina Faso Charge D’Affaires Passida Pascal Gouba a Nijeriya kan kisan gilla da aka yi tare da neman bayanin hakikanin abubuwan da suka faru wajen kisan ‘yan Nijeriya 16 da ake zargin sojojin Burkinabe da aikatawa.

  • Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

A cewarsa, Nijeriya ta damu sosai da wannan lamarin don haka tana bukatar cikin gaggawa a hanzarta samar da amsar tambayoyin da suke yi wa gwamnatin Burkina Faso, a cewar wata sanarwar da hadimin ministan a bangaren yada labarai, Ibrahim Aliyu ya fitar.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ministan ya nuna matukar kaduwarsa kan lamarin tare da misalta hakan da cewa abu ne da ba za a lamunta ba, kuma babu bukatar bata lokaci wajen samu gaskiyar abubuwan da suka faru cikin lamarin. Ya ce, ahlin mamatan su na ta yin tambayoyi daban-daban kuma su na bukatar a gaggauta yin bincike.

 

Ministan ya ce, Nijeriya ba za ta nade hannayenta haka nan tana kallo ana cin zarafi da kashe ‘yan kasarta a sassa daban-daban na duniya ba.

 

A nasa bangaren, ministan harkokin Burkina Faso a Nijeriya, Gouba, ya fara ne a jajanta wa iyalan mamatan tare da gwamnatin Nijeriya hadi da al’ummar kasar bisa abun da ya kira lamari na ban takaici da bakin ciki da ya faru. Ya ce, ya fahimci irin zafi da radadin da iyalan mamatan ke ji.

 

Ya ce, tunin gwamnatin Burkina Faso ta kaddamar da bincike domin ganowa da fito da asalin wadanda suka aiwatar da wannan kisan, ya kara da cewa a shirye suke su yi aiki tare da kwararrun tawaga daga Nijeriya domin gano hakikan abun da ya faru.

 

Daga bisani, Ambasada Dada ya kuma gana da wakilan kungiyar Darikar Tijaniyyah a karkashin jagorancin sakatare-janar na kungiyar Malam Muhammad Alkasim, inda ya masa bayani kan lamarin da ya faru tare da bayani kan ganawarsu da jakadan Burkina Fason.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

Next Post

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Related

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

8 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

10 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

12 hours ago
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba
Manyan Labarai

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

13 hours ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

14 hours ago
Next Post
An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

June 19, 2025
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.