• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Jakadan Burkina Faso Kan Kisan ‘Yan Nijeriya 16

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Jakadan Burkina Faso Kan Kisan ‘Yan Nijeriya 16
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijrtiya ta fara daukan kwakkwaran matakai domin bankado batutuwan da suke mamaye da kisan ‘yan Nijeriya 16 da suka yi niyyar zuwa ziyarar musulunci a Kaolack da ke kasar Senegal da ake zargin jami’an tsaron Burkina Faso ne suka kashe su.

 

Karamin ministan kula da harkokin cikin gida, Ambasada Zubairu Dada shi ne ya gayyaci jakadan na Burkina Faso Charge D’Affaires Passida Pascal Gouba a Nijeriya kan kisan gilla da aka yi tare da neman bayanin hakikanin abubuwan da suka faru wajen kisan ‘yan Nijeriya 16 da ake zargin sojojin Burkinabe da aikatawa.

  • Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

A cewarsa, Nijeriya ta damu sosai da wannan lamarin don haka tana bukatar cikin gaggawa a hanzarta samar da amsar tambayoyin da suke yi wa gwamnatin Burkina Faso, a cewar wata sanarwar da hadimin ministan a bangaren yada labarai, Ibrahim Aliyu ya fitar.

 

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Ministan ya nuna matukar kaduwarsa kan lamarin tare da misalta hakan da cewa abu ne da ba za a lamunta ba, kuma babu bukatar bata lokaci wajen samu gaskiyar abubuwan da suka faru cikin lamarin. Ya ce, ahlin mamatan su na ta yin tambayoyi daban-daban kuma su na bukatar a gaggauta yin bincike.

 

Ministan ya ce, Nijeriya ba za ta nade hannayenta haka nan tana kallo ana cin zarafi da kashe ‘yan kasarta a sassa daban-daban na duniya ba.

 

A nasa bangaren, ministan harkokin Burkina Faso a Nijeriya, Gouba, ya fara ne a jajanta wa iyalan mamatan tare da gwamnatin Nijeriya hadi da al’ummar kasar bisa abun da ya kira lamari na ban takaici da bakin ciki da ya faru. Ya ce, ya fahimci irin zafi da radadin da iyalan mamatan ke ji.

 

Ya ce, tunin gwamnatin Burkina Faso ta kaddamar da bincike domin ganowa da fito da asalin wadanda suka aiwatar da wannan kisan, ya kara da cewa a shirye suke su yi aiki tare da kwararrun tawaga daga Nijeriya domin gano hakikan abun da ya faru.

 

Daga bisani, Ambasada Dada ya kuma gana da wakilan kungiyar Darikar Tijaniyyah a karkashin jagorancin sakatare-janar na kungiyar Malam Muhammad Alkasim, inda ya masa bayani kan lamarin da ya faru tare da bayani kan ganawarsu da jakadan Burkina Fason.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Tattauna Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu

Next Post

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

11 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

13 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

14 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

15 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

16 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

17 hours ago
Next Post
An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.