ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Rabar Da Naira Biliyan 16.1 Ga Masana’antu 22 — Ministan Kudi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
12 months ago
Minista

Gwamnatin tarayyar ta ce, ta rabar da zunzurutun kudade har naira biliyan 16.1 ga masana’antu su 22 da suka kamata daga cikin naira biliyan 75 da gwamnatin ta ware domin ingantawa da bunkasa bangaren.

Kazalika, ta kuma ce a cikin kwana biyar kacal ta rabar da wani karin naira biliyan 3.5 ga wadanda suka ci gajiya su 11,000 daga tsarin tura kudi ga masu bukata ‘Consumer Credit Scheme’, wanda ke da burin cimma ‘yan Nijeriya miliyan 80 domin agaza musu.

Gwamnatin tarayya ta ce mutane miliyan 25 zuwa yanzu suka amfana da tsarin tura kudin kai tsaye ga masu cin gajiya.

ADVERTISEMENT

Wannan bayanan sun fito ne daga bakin ministan kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Wale Edun, wanda ya bayyana a Abuja yayin taron ‘yan kasa da masu ruwa da tsaki kan aiwatar da manufofin da shugaban kasa da ministoci suka gabatar a zangon karshe na 2024.

Ya ce, Nijeriya na bukatar zuba hannun jari na akalla dala biliyan 20 kowace shekara domin samun nasarar zuwa ga muradin inganta tattalin arziki da samun damar inganta matakin ci gaba zuwa kaso 6.3 nan da shekarar 2027.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Da yake sake nanata bukatar zuba hannun jari cikin gaggawa, Mista Edun ya shelanta irin tasirin da zuba hannun jari ke da shi ga jagorantar ci gaban tattalin arziki da bunkasarsa hadi da taimakawa wajen aiwatar da ayyukan raya kasa.

Edun ya ce, “A zahirin gaskiya muna matukar bukatar karin ci gaba. Samun karin dala biliyan 20 duk shekara shi ne burin da muke da shi don samar da ababen more rayuwa da kuma samar da kayan aikin noma.”

Bugu da kari, Edun ya danganta tsarin kasafin kudi da daidaiton farashin musayar kudade su ne za su taimaka wa Nijeriya ta samu janyo hankalin masu zuba hannun jari sosai.

Kazalika, ministan kudin ya ce akwai gayar bukatar amincewa da sabon kudirin garambawul ga haraji, wanda ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa za su amfana daga wannan kudirin gyaran harajin.

Ya roki ‘yan majalisun kasa da su toshe kunnuwansu kawai su amince da kudirin domin amfanunsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Sojoji Za Su Tabbatar Da Manoma Kashi 85 Sun Yi Noma Lafiya A Damina Mai Zuwa – Sanata Yari

Sojoji Za Su Tabbatar Da Manoma Kashi 85 Sun Yi Noma Lafiya A Damina Mai Zuwa - Sanata Yari

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.