• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sa Almajirai Da Yara Fiye Da Miliyan 2 A Karatun Boko

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Sa Almajirai Da Yara Fiye Da Miliyan 2 A Karatun Boko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta sa yara Almajirai fiye da miliyan biyu a makarantar Firamare da koyon Larabci a cikin wata shida.

Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana haka; a lokacin da aka gudanar da taron masu ruwa da tsaki a kan harkokin Ilimi a Nijeriya, ranar Talatar da ta gabata a Abuja.

  • Abubuwan Da Ke Rusa Masana’antun Kiwon Kaji A Nijeriya
  • CISLAC Ta Gudanar Da Taro A Kano Kan Sauyin Yanayi A Nijeriya

Farfesan, ya ce babban abin da ma’aikatar iliminn za ta fi bai wa muhimmanci shi ne, samar da sahihan alkalumma a bangaren, don ci gaban ilimin yara da kuma fasahar koyon abubuwa daban-daban, a haka ne za a iya rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Har ila yau, don kokarin samun nasarar lamarin; ma’aikatar ilimin ta yi tsari mai matukar kyau, wanda aka yi wa lakabi da ‘Tsarin bangaren Ilimi na Nijeriya daga shekarar 2024 zuwa 2027’.

Ministan ya kara da cewa, “Aiwatar da umarnin shugaban kasa ne, ya sa muka gana da masu ruwa da tsaki; don tattauna ci gaban da aka samu dangane da shawarwari 23 da muka cimma.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Haka zalika, daya daga cikin manufofin gwamnati shi ne; kokarin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, wannan dalili ne yasa gwamnati ta himmatu wajen ba wa al’amarin muhimmanci yadda ya kamata.

“Abubuwan da muke bayana sune, irin gudunmawar da hukumomin da ke karkashin ma’aikatar Ilimi ke bayarwa, don kokarin tabbatar da an yi maganin wannan matsala.

Da yake bayani a kan garkuwar da aka yi da daliban Jami’ar Kalaba, Ministan ya ce; ma’aikatar ilimi na aiki tare hukumomin tsaro, domin kokarin samun kubuto da wadannan daliban, sannan kuma hukumar kula da manyan makarantu, ta gina wa jami’ar katanga.

Shi ma a nasa bangaren, Karamin Ministan Ilimi, Dakta Yusuf Sununu ya bayyana kokarin da ma’aikatar ilimi ta yi na shigar da tsarin fasaha a harkar ta Ilimi tare da bunkasa koyon sana’o’i ta bangarori daban-daban.

Sununu ya kara da cewa, hakan zai yi maganin matsalar koyarwa da ake fuskanta a kananan makarantu.

Sannan ya kara jaddada cewa,“Mun sani ko shakka babu, akwai bukatar samar da babbar tawaga wajen maganin matsalolin da ake fuskanta a bangaren ilimi.

Da yake ilimi babban ginshiki ne na rayuwa Dan Adam, al’umma, kasa da kuma duniya baki-daya, shi yasa bai kamata a mayar da shi Saniyar ware ba”.

“Ganin muhimmancin lamarin ne ya sa kungiyar kwadago ta kasa da kasa ta bayyana Ilimi a matsayin kamar wani kaya, da za a iya shigowa da shi, don haka akwai bukatar hadin kan gida da waje; domin cimma wannan buri”.

A nasa banagaren, Kwamishinan Ilimi na Jihar Legas, Jamiu Alli-Balogun ya nuna rashin jin dadinsa da hukumar shirya jarrabawa ta Afirka ta yamma, sakamakon karin kudi da ta yi zuwa Naira 27,000, wanda mafi yawancin iyaye ba za su iya biyan wannan kudi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadace-Fadacen Daba A Birnin Kano: Ina Mafita?

Next Post

Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

7 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

8 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

9 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

14 hours ago
Almajirai
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

14 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

15 hours ago
Next Post
Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.