ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sa Almajirai Da Yara Fiye Da Miliyan 2 A Karatun Boko

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Almajirai

Gwamnatin tarayya ta sa yara Almajirai fiye da miliyan biyu a makarantar Firamare da koyon Larabci a cikin wata shida.

Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana haka; a lokacin da aka gudanar da taron masu ruwa da tsaki a kan harkokin Ilimi a Nijeriya, ranar Talatar da ta gabata a Abuja.

  • Abubuwan Da Ke Rusa Masana’antun Kiwon Kaji A Nijeriya
  • CISLAC Ta Gudanar Da Taro A Kano Kan Sauyin Yanayi A Nijeriya

Farfesan, ya ce babban abin da ma’aikatar iliminn za ta fi bai wa muhimmanci shi ne, samar da sahihan alkalumma a bangaren, don ci gaban ilimin yara da kuma fasahar koyon abubuwa daban-daban, a haka ne za a iya rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, don kokarin samun nasarar lamarin; ma’aikatar ilimin ta yi tsari mai matukar kyau, wanda aka yi wa lakabi da ‘Tsarin bangaren Ilimi na Nijeriya daga shekarar 2024 zuwa 2027’.

Ministan ya kara da cewa, “Aiwatar da umarnin shugaban kasa ne, ya sa muka gana da masu ruwa da tsaki; don tattauna ci gaban da aka samu dangane da shawarwari 23 da muka cimma.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Haka zalika, daya daga cikin manufofin gwamnati shi ne; kokarin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, wannan dalili ne yasa gwamnati ta himmatu wajen ba wa al’amarin muhimmanci yadda ya kamata.

“Abubuwan da muke bayana sune, irin gudunmawar da hukumomin da ke karkashin ma’aikatar Ilimi ke bayarwa, don kokarin tabbatar da an yi maganin wannan matsala.

Da yake bayani a kan garkuwar da aka yi da daliban Jami’ar Kalaba, Ministan ya ce; ma’aikatar ilimi na aiki tare hukumomin tsaro, domin kokarin samun kubuto da wadannan daliban, sannan kuma hukumar kula da manyan makarantu, ta gina wa jami’ar katanga.

Shi ma a nasa bangaren, Karamin Ministan Ilimi, Dakta Yusuf Sununu ya bayyana kokarin da ma’aikatar ilimi ta yi na shigar da tsarin fasaha a harkar ta Ilimi tare da bunkasa koyon sana’o’i ta bangarori daban-daban.

Sununu ya kara da cewa, hakan zai yi maganin matsalar koyarwa da ake fuskanta a kananan makarantu.

Sannan ya kara jaddada cewa,“Mun sani ko shakka babu, akwai bukatar samar da babbar tawaga wajen maganin matsalolin da ake fuskanta a bangaren ilimi.

Da yake ilimi babban ginshiki ne na rayuwa Dan Adam, al’umma, kasa da kuma duniya baki-daya, shi yasa bai kamata a mayar da shi Saniyar ware ba”.

“Ganin muhimmancin lamarin ne ya sa kungiyar kwadago ta kasa da kasa ta bayyana Ilimi a matsayin kamar wani kaya, da za a iya shigowa da shi, don haka akwai bukatar hadin kan gida da waje; domin cimma wannan buri”.

A nasa banagaren, Kwamishinan Ilimi na Jihar Legas, Jamiu Alli-Balogun ya nuna rashin jin dadinsa da hukumar shirya jarrabawa ta Afirka ta yamma, sakamakon karin kudi da ta yi zuwa Naira 27,000, wanda mafi yawancin iyaye ba za su iya biyan wannan kudi ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola
Manyan Labarai

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
Kotu Da Ɗansanda

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Next Post
Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.