ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sa Almajirai Da Yara Fiye Da Miliyan 2 A Karatun Boko

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Almajirai

Gwamnatin tarayya ta sa yara Almajirai fiye da miliyan biyu a makarantar Firamare da koyon Larabci a cikin wata shida.

Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana haka; a lokacin da aka gudanar da taron masu ruwa da tsaki a kan harkokin Ilimi a Nijeriya, ranar Talatar da ta gabata a Abuja.

  • Abubuwan Da Ke Rusa Masana’antun Kiwon Kaji A Nijeriya
  • CISLAC Ta Gudanar Da Taro A Kano Kan Sauyin Yanayi A Nijeriya

Farfesan, ya ce babban abin da ma’aikatar iliminn za ta fi bai wa muhimmanci shi ne, samar da sahihan alkalumma a bangaren, don ci gaban ilimin yara da kuma fasahar koyon abubuwa daban-daban, a haka ne za a iya rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, don kokarin samun nasarar lamarin; ma’aikatar ilimin ta yi tsari mai matukar kyau, wanda aka yi wa lakabi da ‘Tsarin bangaren Ilimi na Nijeriya daga shekarar 2024 zuwa 2027’.

Ministan ya kara da cewa, “Aiwatar da umarnin shugaban kasa ne, ya sa muka gana da masu ruwa da tsaki; don tattauna ci gaban da aka samu dangane da shawarwari 23 da muka cimma.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Haka zalika, daya daga cikin manufofin gwamnati shi ne; kokarin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, wannan dalili ne yasa gwamnati ta himmatu wajen ba wa al’amarin muhimmanci yadda ya kamata.

“Abubuwan da muke bayana sune, irin gudunmawar da hukumomin da ke karkashin ma’aikatar Ilimi ke bayarwa, don kokarin tabbatar da an yi maganin wannan matsala.

Da yake bayani a kan garkuwar da aka yi da daliban Jami’ar Kalaba, Ministan ya ce; ma’aikatar ilimi na aiki tare hukumomin tsaro, domin kokarin samun kubuto da wadannan daliban, sannan kuma hukumar kula da manyan makarantu, ta gina wa jami’ar katanga.

Shi ma a nasa bangaren, Karamin Ministan Ilimi, Dakta Yusuf Sununu ya bayyana kokarin da ma’aikatar ilimi ta yi na shigar da tsarin fasaha a harkar ta Ilimi tare da bunkasa koyon sana’o’i ta bangarori daban-daban.

Sununu ya kara da cewa, hakan zai yi maganin matsalar koyarwa da ake fuskanta a kananan makarantu.

Sannan ya kara jaddada cewa,“Mun sani ko shakka babu, akwai bukatar samar da babbar tawaga wajen maganin matsalolin da ake fuskanta a bangaren ilimi.

Da yake ilimi babban ginshiki ne na rayuwa Dan Adam, al’umma, kasa da kuma duniya baki-daya, shi yasa bai kamata a mayar da shi Saniyar ware ba”.

“Ganin muhimmancin lamarin ne ya sa kungiyar kwadago ta kasa da kasa ta bayyana Ilimi a matsayin kamar wani kaya, da za a iya shigowa da shi, don haka akwai bukatar hadin kan gida da waje; domin cimma wannan buri”.

A nasa banagaren, Kwamishinan Ilimi na Jihar Legas, Jamiu Alli-Balogun ya nuna rashin jin dadinsa da hukumar shirya jarrabawa ta Afirka ta yamma, sakamakon karin kudi da ta yi zuwa Naira 27,000, wanda mafi yawancin iyaye ba za su iya biyan wannan kudi ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Next Post
Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.