ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sa Almajirai Da Yara Fiye Da Miliyan 2 A Karatun Boko

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Almajirai

Gwamnatin tarayya ta sa yara Almajirai fiye da miliyan biyu a makarantar Firamare da koyon Larabci a cikin wata shida.

Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman ne ya bayyana haka; a lokacin da aka gudanar da taron masu ruwa da tsaki a kan harkokin Ilimi a Nijeriya, ranar Talatar da ta gabata a Abuja.

  • Abubuwan Da Ke Rusa Masana’antun Kiwon Kaji A Nijeriya
  • CISLAC Ta Gudanar Da Taro A Kano Kan Sauyin Yanayi A Nijeriya

Farfesan, ya ce babban abin da ma’aikatar iliminn za ta fi bai wa muhimmanci shi ne, samar da sahihan alkalumma a bangaren, don ci gaban ilimin yara da kuma fasahar koyon abubuwa daban-daban, a haka ne za a iya rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, don kokarin samun nasarar lamarin; ma’aikatar ilimin ta yi tsari mai matukar kyau, wanda aka yi wa lakabi da ‘Tsarin bangaren Ilimi na Nijeriya daga shekarar 2024 zuwa 2027’.

Ministan ya kara da cewa, “Aiwatar da umarnin shugaban kasa ne, ya sa muka gana da masu ruwa da tsaki; don tattauna ci gaban da aka samu dangane da shawarwari 23 da muka cimma.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Haka zalika, daya daga cikin manufofin gwamnati shi ne; kokarin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, wannan dalili ne yasa gwamnati ta himmatu wajen ba wa al’amarin muhimmanci yadda ya kamata.

“Abubuwan da muke bayana sune, irin gudunmawar da hukumomin da ke karkashin ma’aikatar Ilimi ke bayarwa, don kokarin tabbatar da an yi maganin wannan matsala.

Da yake bayani a kan garkuwar da aka yi da daliban Jami’ar Kalaba, Ministan ya ce; ma’aikatar ilimi na aiki tare hukumomin tsaro, domin kokarin samun kubuto da wadannan daliban, sannan kuma hukumar kula da manyan makarantu, ta gina wa jami’ar katanga.

Shi ma a nasa bangaren, Karamin Ministan Ilimi, Dakta Yusuf Sununu ya bayyana kokarin da ma’aikatar ilimi ta yi na shigar da tsarin fasaha a harkar ta Ilimi tare da bunkasa koyon sana’o’i ta bangarori daban-daban.

Sununu ya kara da cewa, hakan zai yi maganin matsalar koyarwa da ake fuskanta a kananan makarantu.

Sannan ya kara jaddada cewa,“Mun sani ko shakka babu, akwai bukatar samar da babbar tawaga wajen maganin matsalolin da ake fuskanta a bangaren ilimi.

Da yake ilimi babban ginshiki ne na rayuwa Dan Adam, al’umma, kasa da kuma duniya baki-daya, shi yasa bai kamata a mayar da shi Saniyar ware ba”.

“Ganin muhimmancin lamarin ne ya sa kungiyar kwadago ta kasa da kasa ta bayyana Ilimi a matsayin kamar wani kaya, da za a iya shigowa da shi, don haka akwai bukatar hadin kan gida da waje; domin cimma wannan buri”.

A nasa banagaren, Kwamishinan Ilimi na Jihar Legas, Jamiu Alli-Balogun ya nuna rashin jin dadinsa da hukumar shirya jarrabawa ta Afirka ta yamma, sakamakon karin kudi da ta yi zuwa Naira 27,000, wanda mafi yawancin iyaye ba za su iya biyan wannan kudi ba.

Almajirai
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Almajirai
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Next Post
Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

Jami’ar Bankin Zanaco: Jarin Da Sin Ke Zubawa A Zambia Na Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.