• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan tsaro, Mohammed Abubakar, a daren ranar Alhamis ya sake jaddada aniyar gwamnatin tarayya na magance matsalar ‘yan bindiga da kuma rashin tsaro a fadin Nijeriya baki daya.

 

Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai wa Gwamna Uba Sani ziyara a gidan gwamnatin Sir Kashim Ibrahim da ke Kaduna a wani rangadin da ya ke yi a shiyyar Arewa maso Yamma.

  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 20 Da Kafa Cikakkiyar Dangantakar Abokantaka Bisa Manyan Tsare-tsare Tsakanin Sin Da Italiya A Milan
  • A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Ziyarar dai na da nufin kammala shirye-shiryen kaddamar da shirin ‘Operation Fansar Yamma,’ rundunar hadin gwiwa ta rundunar soji da aka kafa domin magance matsalar rashin tsaro a yankin.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Abubakar, a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala ziyarar, ya jaddada kafa cibiyar gudanarwar tsaro a shiyyar Arewa maso Yamma a matsayin wani muhimmin mataki na magance matsalar ‘yan bindiga da suka addabi yankin.

 

Ministan ya kuma bayyana irin kokarin da gwamnatin kasar ke yi na hadin gwiwa da kasashe makwabta musamman jamhuriyar Nijar wajen yaki da ta’addanci da safarar makamai.

 

A nasa jawabin, a lokacin da yake maraba da Ministan, Gwamna Sani ya jaddada bukatar hadin kan shugabannin yankin domin magance matsalar rashin tsaro.

 

Gwamna Sani ya nuna godiya ga gwamnatin tarayya bisa jajircewar da ta yi na ganin ta magance matsalolin rashin tsaro da ke addabar shiyyar Arewa maso Yamma.

 

Ya kuma bayyana damuwarsa kan illar rashin tsaro a shiyyar Arewa maso Yamma, da suka hada da karancin abinci, karancin hanyoyin kiwon lafiya, da karuwar talauci.

 

Sai dai gwamnan ya bayyana fatansa na cewa, shirin “Operation Fansar Yamma” wanda ake shirin kaddamarwa, zai samar da yanayin zuba jari da bunkasar tattalin arziki a yankin.

 

Gwamnan ya kuma bayar da shawarar mayar da ‘Operation Safe Haven’ da ke Kudancin Kaduna zuwa shiyya ta 1 da ke Kaduna maimakon shiyya ta uku da ke Jos a Jihar Filato domin samun saukin gudanar da ayyuka.

 

Ya yaba da goyon bayan da shugaban kasa Bola Tinubu ke yi bai wa shiyyar Arewa maso Yamma, ya kuma nuna godiya ga Ministan Tsaro, Shugaban Hafsan Tsaro, da Babban Hafsan Soja bisa goyon bayan da suke bai wa yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Yan bindigaYankin Arewa Maso Yamma
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

44 minutes ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

1 hour ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

4 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

6 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

7 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

8 hours ago
Next Post
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.