• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ci Bashin Dala Miliyan 500 Don Gina Hanyoyin Karkara

by Sani Anwar
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya na neman rancen dala miliyan 500 daga Bankin Duniya, don bunkasa hanyoyi da kasuwancin noma a karkara a dukkanin fadin Nijeriya.

Hukumar bayar da lamuni ta kasa da kasa ta ce, ana sa ran wadannan kudade da za a bayar a matsayin rance, za su iya magance matsananciyar bukatar samar da kyakkyawar alaka a yankunan karkarar Nijeriya, inda a halin yanzu kimanin mutane miliyan 92 ke fama da wannan matsala ta hanyoyi.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • Shettima Ya Ƙaddamar Da Ginin Ofishin Hukumar Raya Arewa Maso Gabas

Har ila yau, wannan bukata na kunshe ne cikin wani daftari na musamman da aka samar a hukumance, domin sake kyautata hanyoyi da samar da ayyukan yi ga yankunan karkara da kuma kasuwancin noma, wanda ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya ta samar.

Kazalika, shirin ya mayar da hankali ne wajen inganta hanyoyin shiga yankunan karkara, ta yadda za a inganta noma tare da wayar wa da mutane kai, domin su rungumi harkokin noma a matsayin sana’a don dogaro da kawunansu, wanda hakan ko shakka babu; zai taimaka wajen samar da ingantacciyar rayuwa ga al’ummar karkarar baki-daya.

Haka zalika, makasudin wannan aiki ya hada da inganta hanyoyi da samar da kyakkyawan yanayi a yankunan karkara, karfafa karfin hukumomi don gudanar da hanyoyin sadarwa na yankunan tare kuma da karfafa tushen hanyoyin samun kudi ga hukumomi, domin dorewar ci gaban yankunan karkarar da kuma jihohi.

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Bugu da kari, wannan shiri na samar da hanyoyi da kasuwancin noma a karkara, zai dora ne a kan shirin nan da ake da shi na samar da hanyoyi da kasuwancin noma a karkara, wanda Bankin Duniya da Hukumar Raya Kasar Faransa ke tallafawa. Har ila yau, Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkara ta Tarayya ce ke jagorantar aikin tare da sa ido a sashin kula da ayyukan gwamnatin tarayya.

Haka nan, daftarin ya yi nuni da cewa, “Hanyoyin Nijeriya na da matukar yawa, wanda yawan nasu ya kunshi kusan kimanin kilomita 194,000. Wadannan hanyoyi, sun hada da na gwamnatin tarayya; wadda take titina mai yawan kilomita 34,000, jiha ke da kimanin kilomita 30,000, sai kuma hanyoyin yankunan karkara da aka yi wa rigista kimanin kilomita 130,000.

“Duk da yawan wadannan titina da ake da su, hanyoyin shiga yankuna karkara a Nijeriya, idan aka yi la’akari da yawan al’ummar da ke zaune a cikinsa; za a tarar da cewa, hanyoyin su ne mafi lalacewa da kuma samun koma baya; wanda hakan ya yi sanadiyyar akalla mutane miliyan 92 mazauna karkarar, suka rasa kyawawan hanyoyi kwata-kwata; ta inda ko da noma suka yi, ba sa iya samun damar fitar da amfanin gonar tasu zuwa sauran kasuwanni.

“Kiri-kiri, an hana mutane shiga wadannan yankuna na karkara; musamman yankunan da masu fama da matsalar tattalin arziki suka fi yawa. Don haka, babu shakka wadannan abubuwa na nuna matukar muhimmancin fadadawa tare da inganta hanyoyin wadannan yankuna na karkara da kula da hanyoyin da kuma kadarorin sufurin da ake da su.”

An kiyasta jimillar kudaden wannan aiki a kan dala miliyan 600, wanda ake sa ran Bankin Duniya zai samar da kashi 83.33 cikin 100 na yawan kudaden da ake bukata.

Har ila yau, alkawarin kudaden sun haura kashi 79 cikin 100; sama da adadin da Bankin Duniya ya bayar da farko na dala miliyan 280, don aiwatar da ayyukan da suka shafi iyaye.

Shirin zai dauki nauyin manyan ayyuka guda uku, wadanda suka hada da farfado da hanyoyin karkara (dala miliyan 387), samar da kayayyakin bunkasa sauyin yanayi (dala miliyan 158), sai kuma aikin karfafa cibiyoyin gudanar da ayyuka (dala miliyan 55).

Kamar yadda aka gabatar da tsarin aikin, jihohin da ke son shiga tsarin aikin; wajibi ne su samar da cikakken asusun kula da hanyoyin motoci tare da kafa hukumomi da ma’aikata da kuma tanadar kudaden gudanarwa a cikin kasafin kudin jihar.

Kazalika, tsarin ya tabbatar da cewa, “Cancantar shigar jihohi karkashin wannan tsari, na bukatar tsarawa da kuma sanya kudirin asusun kula da titina a majalisar dokokin jihar. Sannan kuma, sabon aikin zai bukaci jihohi su samar da cikakken asusun kula da titina tare da hukumar kula da titinan da shugabannin gudanarwa da kuma ma’aikata, sai kuma kudaden gudanarwa wanda aka ware a cikin kasafin kudin jihar. Bugu da kari, shirin zai bayar da dama don habaka wakilcin mata a bangaren fannin sufuri.

Don haka, “Za a kasafta kudaden shirin ne bisa gasa tsakanin jihohin da ke samar da kulawa, musamman a bangaren da ya shafi zamantakewar al’umma, domin sake habaka hanyoyi da kuma kara inganta wadatar abinci a yankunan na karkara. Kazalika, za kuma a yi la’akari da jihar da ke nuna jajircewa wajen samar da ingantattun ayyuka gami da yiwuwar samar da kudade daga albarkatun da take da su”.

Haka nan, shirin ya tanadi aiwatar da tsare-tsaren sake inganta rayuwar al’ummar yankunan na karkara, ta hanyar bijiro musu da wadannan sabbin ayyuka; wadanda za su inganta rayuwarsu kai tsaye.

Ana kuma sa ran sama musu wadannan abubuwan alhairi masu matukar muhimmanci da suka rasa tare da tabbatar da ganin an kuma dauki matakan da suka dace, wajen tabbatar da biyan su diyyar filayen da aka karba a hannunsu kafin fara aiwatar da wannan aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiGwamnatin TarayyaTattalin ArzikiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye

Next Post

Firaministan Djibouti Ya Baiwa Rukunin Tallafin Jinya Na Kasar Sin Karo Na 22 Lambar Yabo

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

4 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

2 weeks ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

3 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

3 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 weeks ago
Next Post
Firaministan Djibouti Ya Baiwa Rukunin Tallafin Jinya Na Kasar Sin Karo Na 22 Lambar Yabo

Firaministan Djibouti Ya Baiwa Rukunin Tallafin Jinya Na Kasar Sin Karo Na 22 Lambar Yabo

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.