ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

by Bello Hamza
8 months ago
Jiragen Ruwa

Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, a rabin farkon zangon na shekarar 2025, Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar, sun bayar da gudanwar wajen samun karuwar da ta kai kaso 19.6 a bangaren fitar da kayan da ba su shafi fannin Mai ba.

Kazalika, Dakta Dantsoho ya sanar da cewa, Hukumar ta NPA na kan kokarin ganin cewa, ta samar da tsarin gudanar da yin gasa ta kasa da kasa, musamman domin a kara karfafa gudanar da hada-hadar kasuwanci tare da janyo ‘yan kasuwa daga ketare, da za su zuba hannun jari na kai tsaye da kuma kara karfafa masu guiwa domin dorewar tattalin arzikin kasar, a nan gaba.

  • Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
  • Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Dantsoho ya bayyana hakan ne, a kasidar da ya gabatar a taron Majalisar Dikin Duniya da ake ci gaba da gudanarwa a yanzu a kasar Amurka.

ADVERTISEMENT

Taken kasidar shi ne, ‘ Kula da Kayan Aikin Hukumar Domin a kara Habaka Hada-Hadar Sufurin Jiragen Ruwa da kuma Karfafa Gasa Fadin Duniya.’

Dantsoho ya kara da cewa, a zangon farko na shekarar 2026, Hukumar ta NPA, za ta ci gaba da wanzar da tsarin na Tashar Jiragen Ruwa wato PCS.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

“Muna tabbatar da inganta tsarin na PCS domin a kara tabbatar da karfafa gasa a fadin diniya a fannin na sufurin Jiragen Ruwa na NPA wanda hakan zai kuma kara samar da damar janyo masu zuba hannun jari daga waje na kai tsaye da kuma kara karfafa tattalin arzikin kasar, a nan gaba,”.

A cewarsa, za mu ci gaba da kulla hadaka domin mu cimma burin da aka sanya a gaba, na kara inganta ayyukan Hukumar ta NPA.

Ya ci gaba da cewa, a rabin zangon farko na shekarar 2025, ingancin da aka samar a bangarorin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar sun bayar da gudunmawar da ta karu, zuwa kaso 19.6 a fannin fitar da kaya waje, da ba su shafi fannin mai ba.

Kazalika, Dantsoho ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA, na kan wanzar da tsarin haadaka na fasahar zamani wanda zai sada ya da sauran masu zuba hannun jari da gudanar da hada-hada.

A cewarsa, bisa samar da wannan tsarin na yin amfani da fasar ta zamani, hakan ya taimaka wajen gudanar da hada-hadar a cikin sauki da kuma rage yin asara.

Kazalika, Dantsoho ya bayyana cewa, Hukumar na kuma yin amfani da na’aurar zamani a daukacin harabar ginin na Tashar Jiragen Ruwan da ke a jihar Legas, musamman domin a kara rage cunkoso a Tashar.

“An sanya tsari a cikin yin amfani da na’urar zamani ta ECS wanda hakan ke bayar da damar kula da kayan da ake jigarsu a cikin Jiragen Ruwa zuwa Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar kuma a kan lokaci,” Inji Dantsoho.

Ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA, na gudanar da ayyukanta ne, a zamanance, ba tare da yin amfani da takardun rubutu ba wanda hakan ya taimaka, wajen ragewa Hukumar, yin asara.

Shugaban ya kara da cewa, Hukumar ta NPA, na tabbatar da cewa, ta na ci gaba da kara inganta ayyukanta, inda ya jaddada mahimmancin yin amfani da fasahar zamani domin rage yawan yin dogaro da yin amfani da manyan motocin da ke bin musamman manyan hanyoyin kasar, domin rage fitar da yaki.

Da yake ci gaba da yin tsokaci kan kokarin Hukumar na rage yawan fitar da hayakin na manyan motocin da yeke yin safarar kayan Dantsoho ya sanar da cewa, Hukumar ta ci gaba da kasancewa a gaba wajen gudanar da gangamin ganin an rage yawan hayakin, inda gangamin, ya faro tun daga Tashar Jiragen Ruwa ta Lekki.

“Hukumar ta NPA ta ci gaba da kasancewa a gaba wajen gudanar da gangamin ganin an rage yawan hayakin, inda gangamin, ya faro tun daga Tashar Jiragen Ruwa ta Lekki, “ Inji Dantsoho.

Kazalika, ya bayyana cewa, Hukumar ta kuma himmatu, wajen ganin tana kara zamanantar da ayyuakan da take ci gaba da gudanawar, a daukacin Tashishin Jiragen Ruwa na kasar tare da yin ayyuan, da kayan aiki na zamani, musamman domin a samar da gudanar da yin ayyukan a cikin sauki.

“Wannan babbar Tashar ta Jiragen Ruwa ta Lekki ta hanyar hadaka da NPA da kuma sauran abokan hadaka, da ke a fannin na sufurin Jiragen Ruwa,” Acewar Shugaban.

Shugaban ya ci gaba da cewa, karfin da Tashar ke da shi, ya kai ga har za ta iya tabbatar da gudanar da gasar gudanar da hada-hadar kasuwanci, musamman duba da irin manyan Jiragen Ruwan da ke sauka a Tashar.

“Mun samu damar kaddamarwa da wasu kayan aiki a Tashar ta Lekki ,” Inji Dantsoho.

Jiragen Ruwa
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Fara Aiwatar Da Dokar Sanya Baƙin Gilashi Mota A Legas

Ƴansanda Sun Fara Aiwatar Da Dokar Sanya Baƙin Gilashi Mota A Legas

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.